Gwamnatin Tarayya Ta Tsayar Da Sabon Lokacin Kidaya Yan Najeriya

Gwamnatin Tarayya Ta Tsayar Da Sabon Lokacin Kidaya Yan Najeriya

  • Gwamnatin Najeriya ta dage fara aikin kidiya yan kasa na shekarar 2023 da aka yi shirin farawa a watan Maris zuwa Mayu
  • Alhaji Lai Mohammmed, Ministan Labarai da Al'adu na kasa ne ya bayyana hakan a yau Laraba 15 ga watan Maris bayan taron FEC
  • Mohammed ya ce an dage kidayar jama’a ne saboda sauya jadawalin zaben gwamnoni da na yan majalisar jiha zuwa ranar 18 ga Maris

FCT, Abuja - Gwamnatin Tarayyar Najeriya ta matsar da fara yin aikin kidaya yan kasa na shekarar 2023 zuwa watan Mayun 2023.

Ministan Labarai da Al'adu, Lai Mohammed, a ranar Laraba, ya bayyana hakan a Abuja bayan taron majalisar zartarwa wato FEC da Shugaba Muhammadu Buhari ya jagoranta.

Lai Mohammed
Lai Mohammed ya ce an dage yin kidaya zuwa watan Mayu. Hoto: Ma'aikatar Labarai da Al'adu na Najeriya.
Asali: Facebook

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Kara karanta wannan

Yanzu-Yanzu: Tashin hankali yayin da farashin kayayyaki ya kara hawa a Najeriya daidai karancin Naira

A cewarsa, za a yi kidayar a watan Mayu.

A baya, The Punch ta rahoto cewa za a fara kidayar a ranar 29 ga watan Maris.

Abin da ya sa aka dage yin kidayar ta shekarar 2023 - Lai Mohammed

Ministan ya ce ya zama dole a dage fara aikin kidayar ne saboda sauya ranar yin zabukan gwamnonin jihohi zuwa ranar 18 ga watan Maris.

Mohammed ya ce majalisar zartaswar ta amince a ware naira biliyan 2.8 ga Hukumar Kidayar ta Kasa, NPC, domin ta siyo wasu manhajoji da za a yi amfani da su wurin aikin.

Ya ce:

"Akwai takardar da Hukumar Kidaya ta Kasa ta gabatar na neman siyan wasu manhajoji da za su yi amfani da su wurin kidayar a watan Mayun wannan shekarar. Na yi imanin cewa saboda sauya ranar zabe, ba za su iya fara kidayar kamar yadda aka shirya ba a farko.

Kara karanta wannan

Zaben Gwamnoni: Jerin Jihohi 15 Da PDP Ka Iya Yin Nasara a Zaben Ranar Asabar

"Sun nemi izinin majalisar a bada kwangilar siyo manhajar kidiyar kan kudi naira biliyan 2.8."

Wannan shine kidayar da za a yi bayan shekaru 17 a kasar.

Daily Trust ta rahoto cewa wani ma'aikacin hukumar NPC, wanda ya nemi a sakaya sunansa ya tabbatar da dage fara aikin kidayar.

Ya ce:

"Yanzu za a fara aikin kidayar daga ranar 3 zuwa 7 na watan Mayu kuma shine abin da aka mika wa Shugaban Kasa. Zai amince da hakan amma bai riga ya sa hannu ba."

Shugaba Buhari ya rantsar da mutum 7 da ya ba wa mukami

A wani rahoton kun ji cewa Shugaba Muhammadu Buhari ya rantsar da wasu mutane bakwai da ya sabunta nadinsu a matsayin mambobi na majalisar gudanarwa na hukumar ICPC mai yaki da cin hanci.

Buhari Sallau, hadimin Shugaba Muhammadu Buhari ne ya sanar da hakan a shafinsa na dandalin sada zumunta.

Asali: Legit.ng

Authors:
Aminu Ibrahim avatar

Aminu Ibrahim (Hausa HOD) Aminu Ibrahim leads the Hausa Desk at Legit.ng. He holds a Bachelor's degree in Microbiology from Ahmadu Bello University, Zaria, and pursued further with a Master's degree in Environmental Microbiology from Federal University Dutse, Jigawa. With over seven years of experience, Aminu has honed his craft in news reporting and content editing, weaving narratives that captivate and inspire audiences: aminu.ibrahim@corp.legit.ng or +2348030996164