Kai tsaye: Yadda zaben kananan hukumomin Abuja 6 ke gudana yau Asabar

Kai tsaye: Yadda zaben kananan hukumomin Abuja 6 ke gudana yau Asabar

A yau, 12 ga watan Febrairu 2022, za'a gudanar da zaben kananan hukumomin birnin tarayya Abuja shida.

Sabanin sauran jihohin Najeriya, hukumar INEC da kanta ke gudanar da zaben Abuja.

A bisa alkaluman INEC, mutum 55 ke neman kujeran shugabannin kananan hukumomi yayinda mutumin 363 ke neman kujerar Kansila

Kananan hukumomin sune:

1. Abuja Municipal (Cikin gari)

2. Bwari

3. Kwali

4. Gwagwalada

5. Kuje

6. Abaji

Ka jerin yan takaran:

Na'urar BVAS na aiki yadda ya kamata a Bwari yayinda wasu ke korafi a wasu wurare

An fara zabe a Gwagwalada Abuja

Dattijo ya kada kuriarsa a Gwarimpa

An fara zabe a Bwari Central

Mutane da dama sun fito kada kuri'arsu

An fara zabe a sassan Abuja

AMAC

Akwatin zaben Suncity Estate, AMAC

An fara tantance masu zabe kuma mutumin farko ya kada kuri'arsa. Mutanen da ke nan kalilan ne.

Kuje

An fara tantance masu zabe a fadar Sarki kusa da kasuwar Amebo, Pasali,Kuje.

Amsco Estate Galadimawa

Jami'an INEC sun isa wajen amma babu mutum ko guda da yazo kada kuri'a. Duka-duka mutum 5 akayi rijista a akwatin.

PU 014 Gwarimpa Ward

A makarantar Firamaren Jabi Sariki, an fara tantance masu zabe kuma sun fara kada kuri'unsu.

Online view pixel