Sabbin mutane 1,430 sun kamu da cutar Korona ranar Litinin a Najeriya
- Adadin masu kamuwa da Korona yana karuwa kullum tun da aka shiga sabuwar shekara
- Kusan makonni uku a jere, yan Najeriya sama da 1000 ke kamuwa da Korona kullum
- Gwamnatin tarayya ta yi barazanar sake kafa dokar hana fita idan adadin ya cigaba da karuwa
Ministan Lafiya, Osagie Ehanire, a makon da ya gabata ya bayyana cewa an yi gwajin samfuri milyan daya tun da korona ta bulla a Najeriya kuma sama da dubu dari suka kamu da cutar.
A ranar Litinin, 25 ga watan Junairu 2021, Mutane 1,430 kwayar cutar ta harba a fadin Nigeria kamar yadda alkaluman hukumar hana yaduwar cututtuka NCDC ta saba fitarwa kullum.
Adadin da aka samu ranar Litinin ya kai jimillan wadanda suka kamu da cutar 122,996 a Najeriya.
Daga cikin mutanen da suka kamu, an sallami 98,359 yayinda 1,507 suka rigamu gidan gaskiya.
KU KARANTA: 'Yan sandan Najeriya sun fi na kowace kasa kwarewa a duniya - IGP
Ga jerin wadanda suka kamu a jihohi ranar Litinin:
Lagos-744
Plateau-100
Oyo-77
FCT-75
Nasarawa-74
Katsina-48
Edo-42
Kano-41
Enugu-37
Rivers-34
Ogun-33
Kwara-32
Niger-28
Ebonyi-27
Kaduna-26
Borno-12
Yobe-10
Ekiti-5
Gombe-1
KU KARANTA: Likitoci 3 sun mutu, 53 suna fama da Covid-19 a Kano
A bangare guda, Shugaban hukumar hana yaduwar cututtuka a Najeriya, Chikwe Ihekweazu, ya bayyana cewa amfanin barin yara su koma makaranta ya rinjayi tsoron kamuwa da cutar Korona.
Ihekweazu ya bayyana hakan a taron kungiyar likitocin yaran Najeriya watau (PAN) ranar Juma'a a jihar Legas, The Cable ta ruwaito.
Ihekweazu ya ce lallai ya yi na'am da shawaran bude makarantu.
Domin sauke manhajar labaran Legit.ng a wayar ku ta hannu, latsa wannan rubutu na kasa:
https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa
Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:
Facebook: https://facebook.com/legitnghausa
Twitter: https://twitter.com/legitnghausa
Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,
Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng
Asali: Legit.ng