Sabbin mutane 1,430 sun kamu da cutar Korona ranar Litinin a Najeriya

Sabbin mutane 1,430 sun kamu da cutar Korona ranar Litinin a Najeriya

- Adadin masu kamuwa da Korona yana karuwa kullum tun da aka shiga sabuwar shekara

- Kusan makonni uku a jere, yan Najeriya sama da 1000 ke kamuwa da Korona kullum

- Gwamnatin tarayya ta yi barazanar sake kafa dokar hana fita idan adadin ya cigaba da karuwa

Ministan Lafiya, Osagie Ehanire, a makon da ya gabata ya bayyana cewa an yi gwajin samfuri milyan daya tun da korona ta bulla a Najeriya kuma sama da dubu dari suka kamu da cutar.

A ranar Litinin, 25 ga watan Junairu 2021, Mutane 1,430 kwayar cutar ta harba a fadin Nigeria kamar yadda alkaluman hukumar hana yaduwar cututtuka NCDC ta saba fitarwa kullum.

Adadin da aka samu ranar Litinin ya kai jimillan wadanda suka kamu da cutar 122,996 a Najeriya.

Daga cikin mutanen da suka kamu, an sallami 98,359 yayinda 1,507 suka rigamu gidan gaskiya.

Sabbin mutane 1,430 sun kamu da cutar Korona ranar Litinin a Najeriya
Sabbin mutane 1,430 sun kamu da cutar Korona ranar Litinin a Najeriya Hoto: @NCDCgov
Source: Twitter

KU KARANTA: 'Yan sandan Najeriya sun fi na kowace kasa kwarewa a duniya - IGP

Ga jerin wadanda suka kamu a jihohi ranar Litinin:

Lagos-744

Plateau-100

Oyo-77

FCT-75

Nasarawa-74

Katsina-48

Edo-42

Kano-41

Enugu-37

Rivers-34

Ogun-33

Kwara-32

Niger-28

Ebonyi-27

Kaduna-26

Borno-12

Yobe-10

Ekiti-5

Gombe-1

KU KARANTA: Likitoci 3 sun mutu, 53 suna fama da Covid-19 a Kano

A bangare guda, Shugaban hukumar hana yaduwar cututtuka a Najeriya, Chikwe Ihekweazu, ya bayyana cewa amfanin barin yara su koma makaranta ya rinjayi tsoron kamuwa da cutar Korona.

Ihekweazu ya bayyana hakan a taron kungiyar likitocin yaran Najeriya watau (PAN) ranar Juma'a a jihar Legas, The Cable ta ruwaito.

Ihekweazu ya ce lallai ya yi na'am da shawaran bude makarantu.

Domin sauke manhajar labaran Legit.ng a wayar ku ta hannu, latsa wannan rubutu na kasa:

https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,

Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Authors:
Abdul Rahman Rashid avatar

Abdul Rahman Rashid Rashidah Abdul Rahman 'yar jarida ce kuma dalibar ilimi wacce ta kwashe shekaru kimanin hudu yanzu tare da shararriyar jarida Legit. Ta samu gogewa a ɓangaren rubutun labarai akan fannoni shatta, wanda suka hada da siyasa, kasuwanci, wasanni, nishadi, dss. Zaku tuntubarta a akwatin email: abdulrahman.rashidah@corp.legit.ng