Kazamar siyasa: 'Yan daba dauke da muggan makamai sun kai wa kwamishin Tambuwal hari

Kazamar siyasa: 'Yan daba dauke da muggan makamai sun kai wa kwamishin Tambuwal hari

Wasu 'yan bangar siyasa wadanda ake zargin magoya bayan jam’iyyar APC ne sun kai farmaki a gidan Babban Lauyan Gwamnati kuma Kwamishinan Shari’a na Jihar Sakkwato Barista Sulaiman Usman (SAN) a yammacin jiya tare da muzgunawa jama’a.

Da yake yi wa nanema labarai bayani a Cibiyar Lauyoyi ta Gamzaki a Arkilla, Babban Lauyan Nijeriya, Barista Sulaiman Usman ya bayyana cewar a lokacin da lamarin ya faru yana wajen yakin neman zaben PDP a Karamar hukumar Kware.

Kazamar siyasa: 'Yan daba dauke da muggan makamai sun kai wa kwamishin Tambuwal hari
Kazamar siyasa: 'Yan daba dauke da muggan makamai sun kai wa kwamishin Tambuwal hari
Asali: Twitter

KU KARANTA: Zaben gwamnoni a jahohi 4 da za'a sha gumurzu

A cewar sa 'yan bangar siyasar sun yi aika-aikar ne da hadin bakin wasu jami'an 'yan sandan jihar da kuma wani dan dabar da ake cewa Bashiru Marar-Guiwa.

Kwamishinan ya bayyana cewar wannan ba shine karo na farko ba da hakan ke faruwa domin kuwa hakan ta faru a baya a shekarar 2008 a filin jirgi zai je Abuja daga Sakkwato shekaru 10 da suka gabata.

Daga karshe dai, kwamishinan yayi kira ga Kwamishinan ‘yan sanda da sauran hukumomin tsaro a jihar da su dauki matakin da ya kamata ta hanyar zakulo wadanda lamarin ya shafa tare da hukunta su domin ya zama darasi.

Muhimmiyar sanarwa: Shafin NAIJ.com Hausa ya koma legit.ng Hausa. Mun gode da kasancewarku tare da mu.

Latsa wannan domin samun labarai a wayar ku ta hannu: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://web.facebook.com/legitnghausa?_rdc=1&_rdr

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,

Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.com

Asali: Legit.ng

Authors:
Mudathir Ishaq avatar

Mudathir Ishaq Mudathir Ishaq is the head of the Hausa desk at Legit.ng. He studied Industrial Chemistry as first degree at the University of Abuja, Journalism (CSR Specialization) with the Michigan State University and runs MSc Industrial Chemistry from the Nasarawa State University, Keffi. With more than a decade experience in news reporting and content editing, he has interviewed influential personalities. He can be reached on: mudathir.ishaq@corp.legit.ng