Danjuma-da-Danjummai: 'Yan shi'a sun taya kiristoci bikin kirisimeti a cocin Kaduna
A lokacin bukukuwan Kirsimeti da Kiristoci ke gudanarwa a fadin duniya, almajiran Shaikh Ibraheem Zakzaky da akafi sani da 'yan shi'a sun yi amfani da wannan damar wajen kaiwa Kiristoci ziyarar a cocin ECWA Good News dake Kaduna.
Shugaban Cocin Rabaran Istifanus Isa ya gabatar da wakilin 'yan’uwa a wurin wato Dk. Shu'aibu Musa, inda ya yi jawabi na taya murna da kuma gabatar musu da saƙon Harka Musulunci, da kuma matsayin Kiristoci a wurin mabiya Harkar da sauransu.
KU KARANTA: Atiku ya kada Buhari a wani zaben gwaji
Bayan nan ne, aka gabatar da waƙoƙi daga Ammar Ɗan Tinka da Muhammad Baƙir.
Mahalarta Cocin, sun nuna jin dadinsu sannan sun ce; sun ƙara fahimtar Musulunci ba addinin ta'addanci bane, addini ne na zaman lafiya.
Sun kuma nuna gamsuwarsu da yadda ba a kyamace su har aka zo muhallinsu domin taya su murna.
Muhimmiyar sanarwa: Shafin NAIJ.com Hausa ya koma legit.ng Hausa. Mun gode da kasancewarku tare da mu.
Latsa wannan domin samun labarai a wayar ku ta hannu: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa&hl=en
Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:
Facebook: https://web.facebook.com/legitnghausa?_rdc=1&_rdr
Twitter: https://twitter.com/legitnghausa
Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,
Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.com
Asali: Legit.ng