Barayin da suka yi garkuwa da basarake a Kaduna sun saki matarsa
Masu garkuwan da suka sace matar Shugaban Adara a karamar hukumar Kachia, jihar Kaduna, Misis Victoria Galadima sun sake ta a safiyar ranar Lahadi, 21 ga watan Oktoba.
Da yake tabbatar da sakin nasa, kakakin rundunar yan sandan Kaduna, DSP Yakubu Sabo yace a yanzu haka matar na ganin likita a babban asibitin Kachia.
A cewar sa ana nan ana kokari don tabbatar das akin mijin nata, Dr Maiwada Galadima, wanda ke a hannun masu garkuwa da mutanen har yanzu tare da direbansa wanda aka kira da suna Timothy.

Asali: Depositphotos
Kamfanin dillancin labaran Najeriya (NAN) ya ruwaito cewa mutane hudu harda jami’in dan sanda masu karkuwa da mutanen suka kashe a ranar Juma’a, kafin su tafi da basaraken, matarsa da direbansu.
KU KARANTA KUMA: An kwantar da masoyin Atiku da yayi tattaki daga Owerri zuwa Abuja akan keke a gadon asibiti
A wani lamari na daban, mun ji cewa ‘yan ta'addan Boko Haram sun shiga Kauyukan da ke cikin Garin Konduga a jiya da dare inda su ke cigaba da ta’adi kamar yadda mu ka samu labari daga Hukumar dillacin labarai na kasa watau NAN.
Ba a wuce awa 12 da harin da Boko Haram su ka kai a Yankin Molai da ke cikin Karamar Hukumar Jere ba sai aka ji cewa an sake kai wani danyen hari a Garuruwan Mairari da Femari da ke cikin Jihar Borno inda su kona gidaje.
Idan ka na da wata shawara ko bukatar ba mu labari, a tuntube mu a labaranhausa@corp.naij.com
Ku same mu a https://www.facebook.com/legitnghausa
Ko a http://twitter.com/legitnghausa
Latsa wannan domin samun sabuwar manhajar labarai ta LEGIT NG Hausa a wayar ku ta hannu: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa&hl=en
Asali: Legit.ng