Saraki ya ga uwar bari, ya biya Omo-Agege hakkinsa

Saraki ya ga uwar bari, ya biya Omo-Agege hakkinsa

Rahotanni sun kawo cewa biya Sanata mai wakiltan Delta ta tsakiya, Ovie Omo-Agege dukka hakkinsa bayan majalisar ta dakatar da shi ba bisa ka’ida ba a farkon shekarar nan.

Ci gaban wanda ke zuwa a ranar Alhamis, 18 ga watan Oktoba ya kawo karshen karar da Omo-Agege ya shigar a gaban babbar kotun tarayya kan shugaban majalisar dattawa, Bukola Saraki.

Lauyan Omo-Agege, Dr. Alex Izinyon (SAN), ya sanar da Justis Nnamdi Dimgba a ranar Alhamis cewa an biya wanda yake karewa hakkinsa a ranar 12 ga watan Oktoba, kasa da sa’o’i 24 bayan kotu ta gargadi Saraki akan ya biya bashin ko kuma ya gurfana a gaban kotu.

Saraki ga ji uwar bari, ya biya Omo-Agege hakkinsa
Saraki ga ji uwar bari, ya biya Omo-Agege hakkinsa
Asali: Depositphotos

Justis Dimgba yayi gargadin ne a ranar 11 ga watan Oktoba bayan ya sake ba Sarak damar da zai gyara laifinsa akan zargin da ake masa.

KU KARANTA KUMA: Yanzu Yanzu: An tabbatar da Bindo a matsayin dankarar gwamna na APC a Adamawa

Babban lauyan yace an gabatarwa da sanatan takardan kudi na banki a ranar 12 ga watan Oktoba kuma ya sanya hannu.

Ya kuma bayyana cewa a lokacin da aka gabatar masa da takardan ya lura akwai sauran naira milyan shida inda hadimin shugaban majalisar ya amince da hakan cewa kuskure aka samu wajen na’urar.

A baya Legit.ng ta rahoto cewa an ba sabbin sanatoci daga jihohin Katsina da Bauchi, Ahmed Babba Kaita da Lawal Yahaya Gumau mukaman shugabantar wasu kwamiti daban-daban.

Shugaban majalisar dattawa Bukola Saraki, wanda ya sanar hakan a jiya Laraba, 17 ga watan Oktoba a zangon majalisa, yace Kaita ya zama shugaban kwamitin kasuwanci, yayinda Gumau zai jagoranci shugaban kwamitin kawar da talauci.

Asali: Legit.ng

Authors:
Mudathir Ishaq avatar

Mudathir Ishaq Mudathir Ishaq is the head of the Hausa desk at Legit.ng. He studied Industrial Chemistry as first degree at the University of Abuja, Journalism (CSR Specialization) with the Michigan State University and runs MSc Industrial Chemistry from the Nasarawa State University, Keffi. With more than a decade experience in news reporting and content editing, he has interviewed influential personalities. He can be reached on: mudathir.ishaq@corp.legit.ng