AFCON: ‘Dan Najeriya Ya Yi Hasashen Sakamakon Wasan Karshe Tsakanin Najeriya da Ivory Coast

AFCON: ‘Dan Najeriya Ya Yi Hasashen Sakamakon Wasan Karshe Tsakanin Najeriya da Ivory Coast

  • Hankula sun karkata kan wani 'dan Najeriya, wanda ya yi hasashen cewa Najeriya za ta doke Senegal a a cikin mintuna 90 a soshiyal midiya
  • Ya yada wani bidiyo inda ya tantance makomar Super Eagles tare da bayar da tabbacin cewa Najeriya za ta kaucewa karin lokaci
  • Najeriya za ta so sake yin nasara karo na hudu a gadar AFCON a ranar Lahadi yayin da za ta kara da mai masaukin baki Ivory Coast

Aisha Musa ta shafe tsawon shekaru tana kawo labaran Hausa a bangaren siyasa, tsegumi da al’amuran yau da kullum

Wani 'dan Najeriya ya yi fice a dandalin soshiyal midiya bayan ya yi hasashen yadda karon Najeriya da Ivory Coast za ta kaya a wasan matakin rukuni.

A cikin wani bidiyo da ya wallafa kafin wasan, mutumin ya yi nazarin karfin kungiyar tare da bayyana cewa Najeriya za ta yi nasara a cikin lokaci.

Kara karanta wannan

AFCON: Fitaccen malamin addini ya fadi kasar da za ta yi nasara, sai dai ya ce za a tafka kuskure

'Dan Najeriya ya yi hasashe kan gasar AFCON
AFCON: ‘Dan Najeriya Ya Yi Hasashen Sakamakon Wasan Karshe Tsakanin Najeriya da Ivory Coast Hoto: @thehindsightpod/TikTok
Asali: TikTok

A wani bidiyo da @thehindsightpod ya wallafa, ya ce yana da tabbacin cewa Najeriya ba za ta bukaci karin lokaci ko fenariti ba don yin nasara.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Yanzu Najeriya za ta kara da mai masaukin baki Ivory Coast a wasan karshe a ranar Lahadi, tana mai fatan nasara a karo na hudu a gasar AFCON.

Tuni dai Najeriya ta doke Ivory Coast da ci 1-0 a matakin rukuni, wanda hakan ya bata dama kan abokan karawarta.

Kalli bidiyon a kasa:

Jama'a sun yi martani

Ufiumarfaruk ya ce:

"Wannan mutumin dattijo ne jinjina yallabai."

Dynamic Range:

"Babban mutum!!"

Okeemegor:

"Cikakken lokaci Najeriya 2- 2 Ivory coast. Osimhen zai ci kwallo na uku amma za a soke 1. Wannan shine abin da na gani, zan dawo kan wannan bayan wasan. Oshimhen zai zura kwallo Najeriya za ta yi nasara kan fenariti."

Kara karanta wannan

Tsadar rayuwa: Ta yiwu Tinubu ya rufe iyakar Najeriya kan karancin abinci, ya fadi sauran hanyoyi

SportPremi:

“Ivory Coast 0-2 Najeriya.”

Malami ya fadi kasar da za ta ci gasar AFCON

A wani labarin, mun ji cewa shahararren Fasto, Dakta Kan Ebube Muonso ya yi hasashen kasar da za ta lashe gasar AFCON a gobe Lahadi 11 ga watan Faburairu.

Ebube ya ce kasar Ivory Coast za ta tafi da kofin gida sai dai hakan zai faru ne a cikin kuskure.

Asali: Legit.ng

Authors:
Aisha Musa avatar

Aisha Musa (Hausa writer) Aisha Musa 'yar jarida ce wacce ta kwashe shekaru biyar tana aikin gogewa a harkar yada labarai. Ta kammala karatun ta a Jami'ar Ibrahim Badamasi Babangida (IBB Lapai) a shekarar 2014 tare da digirin farko a fannin Tarihi. Aisha Editan Hausa ce wacce ke amfani da kwarewa da kwazonta don karfafawa wasu gwiwar yin aiki tukuru don cimma nasara. Ta karbi lambar yabo na gwarzuwar shekarar 2021 a bangaren Hausa na Legit. Za ku iya aika mata sakonnin imel ta adireshinta aisha.musa@corp.legit.ng