Hukumar yan sandan NAjeriya
Basarake a Ilawe-Ekiti, Ajibade Olubunmi, ya ce an yi masa barazanar kisa yayin wata ganawar danginsu a ranar 15 ga Maris inda ya yi korafi ga yan sanda.
‘Yan sanda sun kama mutum 12 kan harin masallaci a Rigasa. An ce 'yan daba sun bi wani matashi har cikin masallacin, suka daba masa wuka har lahira ana Sallah.
Wasu miyagun 'yan bindiga sun kai harin ta'addanci kan 'yan sa-kai a jihar Zamfara. 'Yan bindigan sun hallaka jami'an tsaro masu yawa a yayin harin.
Wasu miyagun 'yan bindiga dauke da makamai sun kai harin ta'addanci a babban birnin tarayya Abuja. 'Yan bindigan sun yi awon gaba da wata soja da wasu mutum biyu.
Bayan rigima ta barke a Osun, gwamnatin jihar ta sake kakabawa garuruwan Ifon da Ilobu dokar hana fita daga karfe 6 na yamma zuwa 6 na safe saboda dalilan tsaro.
Sufeton 'yan sandan Najeriya ya yi gargadin cewa za su yi maganin masu son tayar da zaune tsaye a Rivers bayan dakatar da gwamna Siminalayi Fubara.
‘Yan bindiga sun sace dalibai 2 a jami’ar FUDMA, da ke jihar Katsina yayin da aka ceto wani wanda aka yi garkuwa da shi a Adamawa, an kuma kama malami a Jigawa.
‘Yan sanda sun kama masu safarar makamai, miyagun kwayoyi da jabun kuɗi a samame daban-daban, inda suka cafke masu hannu a laifuka tare da kayayyakin haram.
An rahoto cewa Shugaba Bola Tinubu ya saka labule da shugabannin tsaron ne karkashin jagorancin shugaban hafsoshin tsaro, Janar Christopher Musa.
Hukumar yan sandan NAjeriya
Samu kari