Yan bindiga
Dalibai 50 daga makarantar St. Mary’s Papiri sun tsere daga hannun ’yan bindiga a Niger, yayin da daruruwan sauran dalibai da ma’aikata ke tsare a daji.
Yara sun fara barin FGGC Bwari bayan umarnin gwamnati na rufe makarantu 47 saboda barazanar tsaro da yawaitar sace dalibai a Arewa. Iyaye sun yi martani kan hakan.
Gwamnatin jihar Kebbi karkashin jagorancin Gwamna Nasir Idris ta yi wa Sanata Garba Maidoki martani. Ta zarge shi shi da yada bayanan karya kan rashin tsaro.
Jerry Gana ya ce 'yan bindiga na amfani da dalibai a matsayin garkuwa bayan barazanar Trump, yana kira ga gwamnati ta karo haɗin gwiwa da ƙasashen waje.
Wasu 'yan bindiga dauke da makamai sun yi wa jami'an 'yan sanda kwanton bauna a jihar Bauchi. 'Yan bindigan sun hallaka wasu daga cikin jami'an 'yan sandan.
Yobe ta rufe dukkan makarantun kwana a matsayin matakin kare ɗalibai bayan karuwar garkuwa da su a jihohi kamar Kebbi da Neja. Jihohi da dama sun bi sahu.
Gwamnatin jihar Kebbi ta dauki matakin rufe dukkanin makarantu na gwamnati da na kudi saboda rashin tsaro. Ta ce za ta sanar da ranar da za a koma.
‘Yan sanda sun ceto mata da yara 25 a Zamfara yayin da Ministan tsaro, Matawalle ya tabbatar da gano inda aka boye dalibai mata na Kebbi da aka sace.
Sanatan Kebbi ta Kudu a majalisar dattawa, Garba Maidoki ya bayyana bakin cikinsa kan sace dalibai a Maga a jihar yana cewa lamarin ya taba masa zuciya.
Yan bindiga
Samu kari