Tsohon Shugaban APC Ya Fallasa Wanda Ya Jawo Ake Binciken Gwamnatin El Rufai

Tsohon Shugaban APC Ya Fallasa Wanda Ya Jawo Ake Binciken Gwamnatin El Rufai

  • Salihu Muhammad Lukman ya na ganin babu inda Bola Ahmed Tinubu da Uba Sani za su kara motsawa a tafiyar siyasa
  • Tsohon mataimakin shugaban na APC yana ganin fadar shugaban kasa tana da hannu wajen binciken Nasir El-Rufai a Kaduna
  • A wata wasika, Salihu Muhammad Lukman ya fadawa gwamnan Kaduna cewa an kama hanyar ganin bayan mulkinsu a 2027

M. Malumfashi ya shafe shekaru ya na kawo labaran Hausa musamman na siyasa, addini, tarihi, wasanni da al’ada.

Kaduna - Salihu Muhammad Lukman ya yi kaca-kaca da gwamnan jihar Kaduna, Malam Uba Sani, har ya ce ba zai zarce a ofis ba.

Tsohon mataimakin shugaban na jam’iyyar APC yana ganin Bola Tinubu da Uba Sani ba za su yi nasarar komawa kujerunsu a 2027 ba.

Kara karanta wannan

Bayan rasa mulkin Kano, a ƙarshe, Tinubu ya naɗa Nasiru Gawuna mukami

Bola Tinubu da Gwamna Uba Sani
El-Rufai: Salihu Lukman ya soki Bola Tinubu da Gwamna Uba Sani a APC Hoto: Kabiru Garba
Asali: Facebook

Lukman ya kare gwamnatin El-Rufai

The Guardian ta rahoto Salihu Muhammad Lukman yana magana a kan rikicin da Mai girma gwamna Uba Sani yake yi da Nasir El-Rufai.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

‘Dan siyasar yana ganin cewa gwamnan Kaduna yana taya fadar shugaban kasa yakar tsohon gwamnan ne da sunan binciken mulkinsa.

A wata wasika da ya rubuta a ranar 13 ga watan Yuni, Salihu Lukman ya ce tun yanzu an fara shirin kifar da Tinubu da gwamnatin Uba.

Watakila APC za ta rasa zaben 2027

A takardar, Lukman ya gargadi Uba Sani, ya ce ko da ya dace, shekaru bakwai suka rage masa kamar yadda Daily Post ta rahoto a jiya.

Idan har APC ba ta shiga taitayinta ba, ‘dan siyasar ya ce za su yi bakin kokarinsu wajen ganin sun ga bayan jam’iyyar a takarar 2027.

Kara karanta wannan

"Duk da masu ja da ikon Allah, mun yiwa mutanen Kano aiki," Gwamna Abba gida gida

Vanguard ta rahoto Lukman yana zargin Ibrahim Zailani da hannu a binciken gwamnatin El-Rufai tare da taimakon fadar shugaban kasa.

Wadanda aka aikawa wasikar sun hada Mallam Nasir El-Rufai, Ramalan Yero, Rt. Hon. Abbas Tajudeen, B. A. Law-al da Hon. Garba Datti.

Haka kuma an hada da Suleiman Hunkuyi, Yusuf Mairago, Lawal Samaila Yakawada, Bashir Abubakar Alhaji da Mohammed Sani Dattijo.

Uba Sani da gwamnatin Nasir El-Rufai

Ana da labarin ana ganin gwamnatin Uba Sani ta taso Nasir El-Rufai a gaba duk da alakar da ke tsakanin mutanen da suke tsofaffin abokai.

Shehu Usman Adamu bai ganin rigima ake yi a Kaduna, ya ce gwamna da mai gidansa aminai ne har yau, sunnar siyasa ta gaji haka.

Asali: Legit.ng

Authors:
Muhammad Malumfashi avatar

Muhammad Malumfashi (Hausa writer) M. Malumfashi ya samu Digirin farko a ilmin komfuta a ABU Zaria. Baya ga haka ya yi Digirgir a fannin kula da bayanai da wani Digirgir a ilmin aikin jarida duk daga jami'ar. Malumfashi ya kan kawo labaran siyasa, addini, wasanni da al’ada. Ya halarci taron karawa juna sani iri-iri. Imel: muhammad.malumfashi@corp.legit.ng

Online view pixel