Tsoffin Gwamnoni 4 da Sanatocin Arewa 8 a Majalisa da Ba Su Gabatar da Kudiri Ba a Watanni 10

Tsoffin Gwamnoni 4 da Sanatocin Arewa 8 a Majalisa da Ba Su Gabatar da Kudiri Ba a Watanni 10

FCT, Abuja - Tun bayan kaddamar da Majalisar Dattawa ta 10 a watan Yunin 2023, akwai Sanatoci da ba su kawo ko da kudiri guda daya ba.

Abdullahi Abubakar, Editan Legit Hausa ne a bangaren siyasa, kasuwanci da al'amuran yau da kullum ne, ya na da gogewar aikin jarida sama da shekaru uku.

A binciken da Daily Trust ta yi, ta gano cewa akwai tsoffin gwamnoni hudu da Sanatoci 21 da suke ɗumama benci tsawon wannan lokaci.

Akalla akwai tsoffin gwamnonin 13 a Majalisar wanda hudu daga cikinsu ba su yi wani katabus ba tun bayan shigowarsu Majalisar.

Tsoffin gwamnoni da sanatoci a Majalisar Dattawa da ba su gabatar da kudiri ko 1 ba
Tsoffin gwamnoni da sanatoci da ba su gabatar da kudiri ba a Majalisar Dattawa. Hoto: Adams Oshiomole, Rufa'i Hanga, Abdul'aziz Yari.
Asali: Facebook

Tsoffin gwamnoni marasa kudiri a majalisa

Legit Hausa ta jero muku tsoffin gwamnonin da kuma wasu sanatoci da ba su yi abin a zo a gani ba.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Kara karanta wannan

El-Rufai ya shiga sabuwar matsala yayin da majalisar Kaduna ta kafa kwamitin bincike

1. Abdul'aziz Yari - Zamfara ta Yamma (APC)

Sanata Abdul'aziz Yari shi ne tsohon gwamnan jihar Zamfara wanda ya nemi shugabancin Majalisar a bara.

Yari na daga cikin tsoffin gwamnonin da ba su kawo wani kudiri da zai taimakawa al'umma ba, cewar rahoton The Citizen.

2. Adams Oshiomole - Edo ta Arewa (APC)

Tsohon gwamnan jihar Edo, Adams Oshiomole ya daɗe a Majalisar tun bayan barin kujerar shugabancin jam'iyyar APC a Najeriya.

Sai dai sanatan ya tabbatar da cewa ya gama shirya kudirinsa kuma zai gabatar da shi nan ba da jimawa ba.

3. Seriake Dickson - Bayelsa ta Yamma (PDP)

Tsohon gwamnan jihar Bayelsa ya sha rantsuwa a Majalisar ne a watan Yunin shekarar 2023 bayan kammala wa'adinsa na mulkin jihar.

Sanatan na daga cikin tsoffin gwamnonin da suka gaza gabatar da wani kudiri a Majalisar tun bayan kaddamar da ita.

4. Simon Lalong - Filato ta Kudu (APC)

Kara karanta wannan

Mambobin NNPP sun buƙaci Gwamna Yusuf na Kano ya yi murabus cikin sa'o'i 48, ta faɗi dalili

Simon Lalong bai samu zarafin gabatar da wani kudiri ba a Majalisar duk da shafe akalla watanni hudu.

An rantsar da Lalong ne a Majalisar a watan Disambar 2023 bayan samun nasara a Kotun Daukaka Kara.

Sauran sanatocin daga Arewacin Najeriya

1. Tartenger Zam - Benue ta Arewa maso Yamma

2. Kaila Samaila Dahuwa - Bauchi ta Arewa

3. Abdul Ningi - Bauchi ta Tsakiya.

4. Khabeeb Mustapha - Jigawa ta Kudu maso Yamma.

5. Rufai Hanga - Kano ta Tsakiya.

6. Abdulaziz Yar’adua - Katsina ta Tsakiya.

7. Mohammed Dandutse Muntari - Katsina ta Kudu.

8. Peter Jiya - Neja ta Kudu.

Jerin mata da ke Majalisar Dattawa a Najeriya

A baya, mun kawo muku labarin cewa akwai wasu mata da suke cikin Majalisar Tarayya bayan gudanar da zabe a shekarar bara.

A zaben 2023, akwai wasu ‘yan siyasa mata da suka lashe zaben Majalisar Dattawa a Najeriya bayan samun nasara tare da doke maza a zaben.

Legit Hausa ta jero muku cikakken sunayen jajirtattun matan guda hudu da ke Majalisar Dattawa ta 10 a Najeriya.

Asali: Legit.ng

Online view pixel