Kano: NNPP Ta Yi Rashi Bayan Ta Hannun Damar Kwankwaso Ta Yi Murabus Daga Mukaminta

Kano: NNPP Ta Yi Rashi Bayan Ta Hannun Damar Kwankwaso Ta Yi Murabus Daga Mukaminta

  • Ta hannun damar jigon siyasar Kano Sanata Rabiu Musa Kwankwaso ta yi murabus daga kujerar shugabar matan jami'yyar NPP
  • Aisha Ahmed Kaita ta bayyana murabus din nata ne a yau Talata 2 ga watan Afrilu a birnin Kano a yankin Arewa maso Yamma
  • Ta koka kan yadda aka yi watsi da magoya bayanta bayan ba da dukkan gudunmawa wurin kafa gwamnatin jihar

Abdullahi Abubakar, Editan Legit Hausa ne a bangaren siyasa, kasuwanci da al'amuran yau da kullum ne, ya na da gogewar aikin jarida sama da shekaru uku.

Jihar Kano - Shugabar matan jam'iyyar NNPP a Arewa maso Yamma, Aisha Ahmed Kaita ta yi murabus daga mukaminta.

Aisha Kaita ta ajiye aikin ne a yau Talata 2 ga watan Afrilu a birnin Kano saboda wasu dalilai, cewar Punch.

Kara karanta wannan

Sauki ya zo yayin da Dangote ya fara siyar da mai, ya gindaya ka'idoji ga 'yan kasuwa

Shugabar matan NNPP kuma ta hannun daman Kwankwaso ta yi murna
Jigo a tafiyar Kwankwaso kuma shugabar matan NNPP ta yi murabus. Hoto: Rabiu Kwankwaso, Aisha Ahmed Kaita.
Asali: Facebook

Musabbabin murabus din shugabar matan NNPP

Kaita ta ce ta yi murabus din ne a karan kanta kuma har yanzu ta na nan a mambar jami'yyar NNPP, cewar Vanguard.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Sai dai ta koka kan yadda aka yi watsi da magoya bayanta wadanda suka ba da gudunmawa wurin kafa gwamnatin NNPP a jihar.

"Jiya na shaidawa Sanata Rabiu Kwankwaso kudiri na kan ajiye mukamin shugabar matan jam'iyyar NNPP a Arewa maso Yamma."
"Ya tambaye ni ko akwai matsala ne, na ce masa babu komai har yanzu ni mambar jami'yyar ce."

- Aisha Kaita

Kaita Tta ba da tabbacin kasancewarta 'yar NNPP

Ta tabbatar da cewa har yanzu ta na jam'iyyar NNPP kamar yadda ta sanarwa jigon jami'yyar, Sanata Rabiu Kwankwaso.

"Ni cikakkiyar 'yar Kwankwasiyya ce, ina tare da Kwankwasiyya tun a APC da PDP har zuwa NNPP."

Kara karanta wannan

Think Tank: Ƴan Arewa ba za su iya hana Bola Tinubu lashe zaben 2027 ba saboda abu 1

- Aisha Ahmed Kaita

Aisha ta ce sun ba da gudunmawa mai karfi wurin kafa gwamnatin NNPP a Kano amma kuma ko neman shawarinsu ba a yi bare a zo maganan ba da mukamai a gwamnati.

An dakatar da shugabar matan APC

A baya, mun ruwaito muku cewa Jam'iyyar APC a jihar Kaduna ta dakatar da shugabar matan jam'iyyar, Maryam Suleiman.

Jam'iyyar ta dauki matakin ne saboda caccakar Gwamna Uba Sani da ta yi bayan ya yi zargin gadan bashi a jihar.

Wannan na zuwa ne bayan Maryam ta caccaki gwamnan Uba Sani ya yi katobara bayan zargin bashi da gwamnatin Nasir El-Rufai ta bari.

Asali: Legit.ng

Authors:
Abdullahi Abubakar avatar

Abdullahi Abubakar (Hausa editor) Marubuci kuma kwararren ɗan jaridan da ya shafe shekaru 3 yana rubutu a fannin siyasa da harkokin yau da kullum. Ya kammala digirin farko a jami'ar Maiduguri. Ya samu horon aikin jarida a Reuters da AFP, ya sha halartar tarukan karawa juna sani game da bincike da adabi. Tuntube shi a abdullahi.abubakar@corp.legit.ng.