Mutum 8 Da Suka Zama Gwamnoni a Dalilin Hukuncin Kotun Koli Daga 2007 Zuwa Yau
- Kamar yadda kotun koli ta kan tsige Gwamnoni, hakan yana nufin akwai wadanda za a nada a mulki
- A sakamakon hukuncin kotun koli ne aka samu canjin lissafin masu mulki a jihohin Bayelsa da Zamfara
- A shekarun baya, ‘yan adawa sun karbe mulki daga hannun jam’iyyar PDP a Edo, Osun, Ekiti da sauransu
M. Malumfashi ya shafe shekaru ya na kawo labaran Hausa musamman na siyasa, addini, tarihi, wasanni da al’ada.
Abuja - An yi ‘yan siyasa da suka zama gwamnoni a sanadiyyar hukuncin kotun koli wanda ita ce kotu mafi girma a dokar Najeriya.
A rahoton nan, Legit ta tattaro ‘yan siyasan da suka yi sa’ar samu mulki ta hanyar kotu:

Asali: Getty Images
Su wanene gwamnonin kotun koli?
1. Peter Obi
LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng
Peter Obi ya koma kan kujerar mulkinsa a jihar Anambra ne da alkalan kotun koli suka tsige Mai girma Andy Uba a tsakiyar shekarar 2007.
2. Adams Oshiomhole
Adams Oshiomhole ya yi mulki a jihar Edo ne da kotu ta tunbuke Farfesa Oserheimen Osunbor bayan 'yan watanni a ofis a matsayin gwamna.
3. Kayode Fayemi
Dr. Kayode Fayemi yana sahun nan domin a dalilin tsige Olusegun Oni a kotu ne ya samu mulki, ya yi shekaru hudu a ofis kafin a doke shi a 2014.
4. Rauf Aregbesola
Osun ta na cikin jihohin da PDP ta rasa bayan zaben 2007, Rauf Aregbesola ya yi nasara a kotun koli a kan Mai girma Olagunsoye Oyinlola.
5. Bello Matawalle
Mukhtar Idris ake shirin za a rantsar a matsayin gwamna sai kotun koli ta karbe kujerun APC a Zamfara, a haka Bello Matawalle ya dare mulki
6. Hope Uzodinma
A zaben 2019, hukumar INEC ta ba Emeka Ihedioha nasara ne amma daga baya alkalai suka ce Hope Uzodinma na APC ne halattacen gwamna.

Kara karanta wannan
Yanzun Nan: Babbar Kotu ta yanke hukunci kan tsohon ministan da ake zargi da karkatar da $6bn
7. Douye Diri
Douye Diri ya sha kashi a hannun David Lyon a zaben gwamnan Bayelsa, kwatsam ana shirin rantsar da APC sai kotun koli ta soke nasarar Lyon.
8. Rotimi Amaechi
Rotimi Amaechi ya samu mulki ne a irin haka a 2007, duk da ba shi ya shiga zaben gwamnan Ribas ba, kotu ta ba shi nasara a jam’iyyar PDP.
Yadda Bola Tinubu ya samu mulki
A makon nan aka ji labari Femi Gbajabiamila ya fadi yadda aminan Bola Tinubu suka yi sanadiyyar zamansa shugaban kasa a 2023.
Hadimin fadar shugaban kasan ya ce wadanda suka yi aiki da Bola Tinubu a 1992 sun yi masa rana da ya tsaya takara a inuwar APC.
Asali: Legit.ng