To Fa: Manyan Jiga-Jigai Sun Matsa a Sauke Gwamnan APC a Ɗora Mataimakinsa a Matsayin Gwamna
- Masu ruwa da tsaki na APC a jihar Ondo sun jaddada buƙatar a baiwa mataimakin gwamna karfin muƙaddashin gwamna
- A cewarsu, tsawon lokacin da aka ɗauka ba tare da Gwamna Akeredolu ya koma ofis ba ya kara kara ruguza tattalin arziƙin jihar
- Wannan na zuwa ne bayan Shugaba Bola Tinubu ya bukaci kowane ɓangare ya sassauta kowa ya tsaya a matsayinsa
Ahmad Yusuf, kwararren edita ne a Legit Hausa da ya shafe tsawon shekaru yana kawo muku rahotannin siyasa, nishadi da al'amuran yau da kullum
Jihar Ondo - Wasu manyan jiga-jigai da kusoshin jam'iyyar APC a jihar Ondo sun jaddada cewa ya kamata a ɗora mataimakin gwamnan jihar, Lucky Aiyedatiwa, a kujerar muƙaddashin gwamna.
![Mataimakin gwamnan jihar Ondo, Lucky Aiyedatiwa. Mataimakin gwamnan jihar Ondo, Lucky Aiyedatiwa.](https://cdn.legit.ng/images/1120/886c91024f2916af.jpeg?v=1)
Asali: Facebook
Kamar yadda jaridar The Nation ta ruwaito, jagororin APC sun bukaci a ayyana Mista Aiyedatiwa a matsayin muƙaddashin gwamnan Ondo kamar yadda kundin tsarin mulki ya tanada.
![](https://cdn.legit.ng/images/360x203/5880e6a3ab7ff2e8.jpeg?v=1)
Kara karanta wannan
Ganduje ya kinkimo babban aiki a APC, ya fara shirin kwace wata jiha 1 daga hannun PDP
Idan baku manta ba, shugaban kasa, Bola Ahmed Tinubu, ya shiga tsakani da nufin kawo karshen rikicin siyasar da ya barke tsakanin gwamna da mataimaki.
LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng
A ranar Juma’a, Shugaba Bola Tinubu ya nemi kowane ɓangare ya maida wuƙarsa kube kuma Aiyedatiwa ya koma ofishinsa a matsayin mataimakin gwamna, in ji rahoton Leadership.
Amma masu ruwa da tsakin APC na Ondo, a wani taro da suka yi a Akure, sun ce dagon lokacin da aka ɗauka ba tare da Gwamna Oluwarotimi Akeredolu ya koma Ofis ba ya gurgunta tattalin arzikin jihar.
Wace matsaya kusoshin APC suka cimma a taron?
A wata sanarwa da suka fitar bayan taron mai ɗauke da sa hannun shugaba, Afe Olowookere, da sakatare, Raman Rotimi, masu ruwa da tsakin sun aike da saƙo ga majalisar dokoki.
![](https://cdn.legit.ng/images/360x203/a62154a47354975b.jpeg?v=1)
Kara karanta wannan
Shugaba Tinubu ya gana da Ganduje da gwamnoni uku, ya musu nasihar yadda zasu ɗauki talakawa
Sun nemi majalisar ta ayyana mataimakin gwamna, Aiyedatiwa a matsayin muƙaddashin gwamna kafin gwamnan ya gama warkewa.
Sun kuma yanke shawarin cewa ya kamata uwar jam'iyyar APC ta ƙasa ta ƙara zage dantse wajen jan kowa a jiki da mutunta kowa.
Wani sashin sanarwan ya ce:
"Bisa haka ya kamata a riƙa baiwa mambobin jam'iyyar APC dama wajen zaɓen waɗanda zasu rike muƙaman siyasa da na cikin jam'iyya."
Jiga-jigan NNPP na fuskantar barazana
A wani rahoton kuma Jam'iyyar NNPP ta bankaɗo wani rahoto na barazanar da ake yi wa jiga-jiganta da nufin ganin bayansu.
A wasiƙar da ta aike ga IGP, NNPP ta ce wasu da ake wa laƙabi da yan bindigan da ba'a sani ba na shirin kai hari sakateriyar jam'iyya.
Asali: Legit.ng