Tsohon Jigo Ya Fadi Barazanar da Takarar Atiku Ta ke Fuskanta Daga Jagororin PDP

Tsohon Jigo Ya Fadi Barazanar da Takarar Atiku Ta ke Fuskanta Daga Jagororin PDP

  • Umar Ardo ya bayyana cewa duk da Atiku Abubakar ne ya rike tutar PDP a 2019 da 2023, yana da jan aiki gaban shi
  • ‘Dan siyasar wanda ya fito daga jihar Adamawa ya nuna Nyesom Wike ya yi karfi a PDP bayan zaben 2015 zuwa yanzu
  • Kafin Atiku ya sauya-sheka daga APC zuwa PDP a 2017, Dr. Ardo ya ce Gwamnoni sun yi karfi a jam’iyyar adawar

M. Malumfashi ya shafe shekaru ya na kawo labaran Hausa musamman na siyasa, addini, tarihi, wasanni da al’ada.

Abuja - Umar Ardo fitaccen ‘dan siyasa ne a Arewacin Najeriya, ya na cikin wadanda aka rika rikici da su a jam’iyyar PDP a shekarun nan.

Punch ta samu lokaci ta yi hira da Dr. Umar Ardo, ta tattauna da shi a kan rikicin PDP, sauya-shekarsa da kuma mulkin Muhammadu Buhari.

Kara karanta wannan

Wasu sun tsinke da lamarin Tinubu da Kotu ta tsige gwamnonin adawa 3 a kwana 4

A hirar da aka yi da ‘dan siyasar, ya nuna cewa jagororin jam’iyyar PDP ba su tare da Atiku Abubakar duk da ya samu tikitin zaben 2023.

Atiku
'Dan takaran PDP a 2023 Hoto: Atiku Abubakar
Asali: Facebook

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Manyan PDP na goyon bayan Atiku?

"Ba na tunani mafi rinjayen shugabannin jam’iyyar suna tare da Atiku Abubakar har yanzu.
Ka da a manta Atiku ya dawo PDP ne a 2017, bayan ya tafi APC, a lokacin da Nyesom Wike a matsayin gwamna ya na rike da jam’iyyar.
Shi (Wike) ne ya kori Ali Madu Sheriff daga shugaban jam’iyya, kuma shi ne a Fatakwal ya kawo kwamitin rikon kwaryan Ahmad Makarfi."

- Dr. Umar Ardo

Nyesom Wike ya fi Atiku karfi a PDP?

Dr. Ardo yake cewa bayan Wike ya yi sanadiyyar kawo Makarfi sai Uche Secondus ya zama shugaban jam’iyya, Atiku bai san ana yi ba.

Kara karanta wannan

Dalilai 4 da suka sa Anyanwu na PDP ya fadi zaben gwamnan Imo na 2023

Kamar yadda ya fada, gwamnoni suna da karfi a PDP har ta kai sun ba Atiku sharadin sai ya goyi bayan wasu ‘yan takaransu a jihohi.

Tsohon jagoran na PDP ya ce a haka aka kakabawa Atiku Amadu Fintiri a Adamawa, kwanaki aka ji shi ya taya Wike murnar zama Minista.

Yadda Atiku Abubakar ya samu tikitin PDP

"Kun ga rawar da Wike ya taka a tsige Secondus, duk da ya saba doka, aka kawo Ayu.
Atiku ya samu takarar shugaban kasa a 2019 da 2023 ne saboda wasu abubuwa da su ka yi tasiri a wajen siyasar cikin gidan jam’iyyar PDP."

- Dr. Umar Ardo

Atiku yana so a hada-kai kafin 2027

Jam’iyya mai alamar kayan dadi za ta iya kawo cikas wajen haduwar PDP, LP da NNPP kamar yadda labari ya gabata a makon da ya gabata.

Atiku Abubakar ya fara kiran ‘yan adawa su yi wa jam’iyyar APC taron dangi, amma NNPP ta nuna dole a ba Rabiu Kwankwaso tikitin yin takara.

Asali: Legit.ng

Authors:
Muhammad Malumfashi avatar

Muhammad Malumfashi (Hausa writer) M. Malumfashi ya samu Digirin farko a ilmin komfuta a ABU Zaria. Baya ga haka ya yi Digirgir a fannin kula da bayanai da wani Digirgir a ilmin aikin jarida duk daga jami'ar. Malumfashi ya kan kawo labaran siyasa, addini, wasanni da al’ada. Ya halarci taron karawa juna sani iri-iri. Imel: muhammad.malumfashi@corp.legit.ng