Kai Tsaye: Kotun Koli Ta Fara Sauraron Daukaka Karar Atiku, Obi Kan Nasarar Tinubu
Kotun ƙoli ta ɗage ɗaukaka ƙarar PDP/LP
Kotun ƙoli mai alƙalai bakwai a ƙarƙashin jagorancin mai shari’a Okoro ta dage zaman bayan ƙarar bayan muhawarar lauyoyin PDP da LP.
"Wannan ɗaukaka ƙarar an tanada hukunci har zuwa ranar da za a sanar da bangarorin," A cewar Okoro.
Kotun koli ta tanadi hukunci a ƙarar Obi/LP
Kotun ƙoli ta tanadi hukunci a ƙarar da Peter Obi da jam'iyyar Labour (LP) suka shigar. Mai shari’a Okoro ya ce za a sanar da ɓangarorin biyu idan hukunci ya kammalu.
Lauyan wadanda suka shigar da ƙara, Livy Uzoukwu (SAN), yayin da yake gabatar da rubutaccen bayaninsa, ya roki kotun da ta amince da buƙatun da suka nema a ƙarar.
Lauyoyin masu kare waɗanda ke ƙara, Abubakar Mahmoud (SAN) na INEC, Wole Olanipekun (SAN) na Tinubu da mataimakin shugaban ƙasa Kashim Shettma da Akin Olujinmi (SAN) na jam'iyyar APC sun buƙaci kotun da ta yi watsi da ƙarar saboda rashin cancanta.
Kotun koli ta yi watsi da ƙarar da APM ta ɗaukaka
Kotun ƙoli ta yi watsi da ƙarar da jam'iyyar Allied Peoples Movement (APM) ta shigar.
Ƙarar dai tana ƙalubalantar zaɓen Kashim Shettima a matsayin ɗan takarar mataimakin shugaban ƙasa na jam’iyyar APC.
Kotun da Okoro yake jagoranta ta yi watsi da ƙarar bayan lauyan wanda ya shigar da kara, Chukwuma Majukwu Umeh, ya nemi janye karar.
Kotun ta kuma yi nuni da cewa ƙarar ba ta da tushe balle makama domin a baya kotun ƙoli ta yi hukunci a shari'ar DP da INEC da sauransu, mai cewa an bi ƙa'ida wajen zaɓo Kashim Shettima.
Kotu ta fara sauraron ƙarar jam'iyyar APM
Kotun ƙoli ta sake dawowa domin saurarin ɗaukaka ƙarar da jam'iyyar Allied Peoples Movement (APM) ta yi.
Kotu ta tanadi hukunci kan karar Atiku/PDP
Kotun koli ta tanadi hukunci a kan ƙarar da Atiku da PDP suka shigar.
Kotun mai alƙalai bakwai ƙarƙashin jagorancin mai shari’a Okoro, ta sanar da matakin ne bayan lauyoyin da ke kare ɓangarorin gabatar da bayanansu na ƙarshe.
Legit.ng ta tattaro cewa kotun ƙolin ta kuma saurari mahawara daga lauyoyin ɓangarorin a kan buƙatar da masu ɗaukaka ƙara suka shigar na kawo sabbin shaidu.
Tawagar lauyoyin Atiku a ƙarƙashin jagorancin Chris Uche (SAN), ta bukaci kotun da ta amince da bukatar ta da kuma soke cancantar Shugaba Tinubu.
Lauyoyin da waɗanda ake ƙara, Abubakar Mahmoud, SAN (INEC), Cif Wole Olanipekun, SAN (Tinubu) da Cif Akin Olujinmi, SAN (APC) sun buƙaci kotun da ta yi watsi da buƙatar da ɗaukaka ƙarar saboda rashin cancanta.
Ganduje, Ribadu, Gbajabiamila sun hallara a kotun koli
Yayin da ake shirin fara sauraran kararrakin zaben shugaban kasa, shugaban jam'iyyar APC, Abdullahi Ganduje ya samu halartar kotun.
Sauran wadanda su ka hallara a kotun sun hada da mai ba da shawara a harkokin tsaro, Nuhu Ribadu da Sakataren Gwamnatin Tarayya, Femi Gbajabiamila da sauransu.
Sauran
Kotun koli ta fara sauraron ƙara
Kotun Koli a yanzu ta fara sauraron ƙararraki uku da ke ƙalubalantar nasarar Shugaba Tinubu.
Kotun ƙolin ta fara da sauraron ɗaukaka ƙarar Atiku Abubakar da jam'iyyar Peoples Democratic Party (PDP).
Mai shari’a John Okoro ne ke jagorantar alƙalai bakwai na kotun ƙolin da ke sauraron ƙararrakin.
Manyan lauyoyi sun iso kotun koli a Abuja
Manyan lauyoyi sun samu isowa zuwa kotun koli don fara shirin sauraran kararrakin zaben shugaban kasa.
Manyan lauyoyin sun hada da ma su kare jam'iyyar PDP da APC da kuma APM.