Shugaba Tinubu Ya Nada Tsohon Ministan Buhari Matsayin SGF

Shugaba Tinubu Ya Nada Tsohon Ministan Buhari Matsayin SGF

  • Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya tabbatar da nadin tsohon minister Dakta George Akuma a matsayin Sakataren Gwamnatin Tarayya, SGF
  • Hakan na zuwa ne jim kadan bayan nada Kakakin Majalisar Tarayya Mr Femi Gbajabiamila a matsayin shugaban fadar ma'aikatan shugaban kasa
  • Shugaban na Najeriya kuma ya sanar da nada Sanata Ibrahim Hassan Hadejia, tsohon mataimakin gwamnan jihar Jigawa, a matsayin mataimakin shugaban ma'aikatan fadar shugaban kasa

Fadar Shugaban Kasa, Abuja - Shugaba Bola Ahmed Tinubu, a ranar Juma'a, 2 ga watan Yuni, ya sanar da nadin tsohon Ministan Ayyuka Na Musamman, Dakta George Akume, a matsayin Sakataren Gwamnatin Tarayya.

Tsohon gwamnan na jihar Benue ya yi aiki a karkashin gwamnatin Shugaba Kasa Muhammadu Buhari a matsayin ministan ayyuka na musamman.

Tinubu ya nada George Akume matsayin SGF
Tinubu ya nada tsohon minista, Sanata George Akume a matsayin Sakataren Gwamnatin Tarayya. Hoto: Photo credit: Senator Dr. George Akume
Asali: Facebook

An tabbatar da nadin Dakta George Akume a matsayin sakataren gwamnatin tarayyar Najeriya (SGF)

Kara karanta wannan

Da Dumi-Dumi: An Hangi Wike, Makinde, Ibori A Aso Rock, Sunyi Muhimmin Taro Da Shugaba Tinubu

Tsohon hadimin Shugaba Muhammadu Buhari, Tolu Ogunlesi, ne ya sanar da hakan cikin wata sako da ya wallafa a shafinsa na Twitter.

Shin kana da labarin da ka/ki ke son an wallafa ma ka/ki? Ka tuntubemu a info@corp.legit.ng!

Sakon da Legit.ng Hausa ta gani ya ce:

"PBAT ya yi nade-nadensa na farko:
"Shugaban Fadar Ma'aikatan Shugaban Kasa, @femigbaja
"Mataimakin Shugaba Fadar Ma'aikatan Shugaban Kasa: Sanata Ibrahim Hassan Hadejia, tsohon mataimakin gwamnan jihar Jigawa
"Sakataren Gwamnatin Tarayya (SGF): Tsohon Ministan Ayyuka na Musamman, George Akume.
"A al'adar Najeriya, Mataimakin Shugaban Fadar Shugaban Kasa yana yi wa mataimakin shugaban kasa aiki ne."

Muhimman Abubuwa 7 Da Ya Dace Ku Sani Game Da Ministan Buhari Da Tinubu Ya Nada SGF

A yau Juma'a 2 ga watan Yuni ne Shugaban Kasa Bola Ahmed Tinubu ya sanar da nadin Sanata George Akume, tsohon ministan harkokin na musamman a gwamnatin Buhari don zama Sakataren Gwamnatin Tarayya.

Kara karanta wannan

Sabuwar Gwamnati: Jerin Sunayen Wadanda Tinubu Ya Ba Wa Mukami a Makonsa Na Farko

Dakta George Akume kuma ya taba yin gwamna a jihar Benue a 1999 inda ya yi mulki na wa'adi guda biyu a jihar da ke arewacin Najeriya.

Bayan ya kammala wa'adinsa a matsayin gwamna a shekarar 2007, Akume ya yi takarar sanatan Arewa maso yammacin Benue, inda daga bisani ya zama shugaban masu rinjaye a majalisar a wani lokaci.

Baya gaza zarcewa a majalisa a 2019 ne Shugaba Buhari ya nada shi ministan ayyuka na musamman.

Asali: Legit.ng

Authors:
Aminu Ibrahim avatar

Aminu Ibrahim (Hausa HOD) Aminu Ibrahim leads the Hausa Desk at Legit.ng. He holds a Bachelor's degree in Microbiology from Ahmadu Bello University, Zaria, and pursued further with a Master's degree in Environmental Microbiology from Federal University Dutse, Jigawa. With over seven years of experience, Aminu has honed his craft in news reporting and content editing, weaving narratives that captivate and inspire audiences: aminu.ibrahim@corp.legit.ng or +2348030996164