Masari ya nada Muntari Lawal a matsayin mukaddashin sakataren gwamnatin jihar Katsina

Masari ya nada Muntari Lawal a matsayin mukaddashin sakataren gwamnatin jihar Katsina

  • Gwamna Aminu Bello Masari ya nada Alhaji Muntari Lawal a matsayin mukaddashin sakataren gwamnatin jihar Katsina
  • Hakan ya biyo bayan ajiye aiki da sakataren gwamnatin jihar, Dr Mustapha Inuwa, ya yi domin ya samu damar shiga takarar kujerar gwamna a zaben 2023
  • Ana tsammanin Masari zai yi karin nade-nade a yan kwanaki masu zuwa domin cike gurbin da wasu mambobin majalisarsa suka bari

Katsina - Gwamnan jihar Katsina, Aminu Bello Masari, ya nada Alhaji Muntari Lawal a matsayin mukaddashin sakataren gwamnatin jihar.

Daily Trust ta rahoto cewa sabon nadin na kunshe ne a cikin wata sanarwa dauke da sa hannun darakta janar na labaran gwamnan, Al-Amin Isa.

Nadin nasa ya biyo bayan murabus din sakataren gwamnatin jihar, Dr Mustapha Inuwa, wanda ya shiga takarar kujerar gwamnan jihar a zaben 2023.

Kara karanta wannan

Shirin 2023: kwamishinan gwamna Zulum ya yi murabus, zai tsaya takara kujerar yankinsu

Masari ya nada Muntari Lawal a matsayin mukaddashin sakataren gwamnatin jihar Katsina
Masari ya nada Muntari Lawal a matsayin mukaddashin sakataren gwamnatin jihar Katsina Hoto: Vanguard
Asali: Facebook

Kafin nadin nasa a sabon mukamin, Lawal ya kasance shugaban ma’aikatan gwamnan.

Shin kana da labarin da ka/ki ke son an wallafa ma ka/ki? Ka tuntubemu a info@corp.legit.ng!

Vanguard ta rahoto cewa nadin nasa ya fara aiki ne a nan take.

A yan kwanaki masu zuwa, ana sa ran gwamnan na jihar Katsina zai yi Karin nade-nade domin cike gurbin da mambobin majalisarsa da ke shirin tsayawa takarar kujerun siyasa a zabe mai zuwa suka bari.

Shirin 2023: Ali Ndume, Suswam da jiga-jigai 5 da ke aiki don ganin wasu 'yan takara sun gaji Buhari

A gefe guda, mun ji cewa yayin da Najeriya ke shirye-shiryen babban zabenta na 2023, wasu yan siyasa sun nada wadanda za su jagoranci yakin neman zabensu.

Yan siyasa a fadin jam’iyyun siyasa daban-daban suna ta tallata ubannin gidansu domin ganin sun zama yan takarar jam’iyyunsu mabanbanta.

Kara karanta wannan

Katsina: Sakataren gwamnati ya yi murabus daga kan mukaminsa, ya shiga takara a 2023

A cikinsu akwai manyan sanatoci, gogaggun ‘yan siyasa da kuma tsofaffin masu rike da mukaman siyasa.

Asali: Legit.ng

Online view pixel