Sunaye: Gwamnan Kano, Abba Ya Nada Mutum 19 Masu Taimaka Masa na Musamman

Sunaye: Gwamnan Kano, Abba Ya Nada Mutum 19 Masu Taimaka Masa na Musamman

  • Gwamna Abba Kabir Yusuf ya amince da naɗin ƙarin manyan mataimaka na musamman (SSA) 19 don ƙarfafa shugabanci a Kano
  • Daga cikin wadanda aka nada akwai Sunusi Kata Madobi, matsayin SSA na Rediyo I, wanda zai maye gurbin marigayi Abdullahi Tanka
  • Gwamna Abba Yusuf na fatan sababbin hadiman za su yi amfani da ƙwarewarsu wajen ba da gudunmawa ga ci gaban jihar Kano

Sani Hamza, kwararren edita ne a fannin nishadi, al'amuran yau da kullum da kuma siyasa. Sani yana da shekaru sama da biyar a aikin jarida

Kano – Gwamnan jihar Kano, Alhaji Abba Kabir Yusuf, ya amince da naɗin ƙarin manyan mataimaka na musamman (SSA) guda 19.

Wannan nadin na daga cikin matakan da Gwamna Abba Yusuf yake dauka domin ƙara ƙarfafa shugabanci da inganta isar da ayyukan ga al’ummar jihar.

Gwamna Abba Yusuf ya nada sababbin manyan masu taimaka masa 19 a ranar Juma'a
Gwamnan jihar Kano, Mai Girma Abba Kabir Yusuf. Hoto: @Kyusufabba
Source: Facebook

Gwamna Abba ya nada manyan hadimai 19

An tabbatar da wannan nadin ne a cikin wata sanarwa da mai magana da yawun gwamnan, Sanusi Bature Dawakin Tofa, ya fitar a shafinsa na Facebook a ranar Juma’a.

Kara karanta wannan

Kano Pillars: Kyaftin Ahmed Musa ya samu babban mukami a gwamnatin Abba Gida Gida

Naɗin waɗannan mataimaka na musamman na nuni da ci gaba da ƙoƙarin gwamnatin Kwankwasiyya a Kano na tabbatar da ingantaccen mulki da ya dace da buƙatun al’umma.

Sanarwar Sanusi Bature Dawakin Tofa ta ce:

"Gwamnan jihar Kano, Alhaji Abba Kabir Yusuf, ya amince da naɗin ƙarin manyan masu taimaka masa na musamman (SSA) domin ƙarfafa shugabanci da inganta isar da ayyuka a jihar."

Sunayen sababbin hadiman gwamnan Kano

An raba muƙaman ga sababbin hadiman kamar haka:

S/N

Sunaye

Mukami

Wurin Aiki

1

Hon. Sunusi Kata Madobi

Babban mataimaki na musamman (SSA)

Rediyo I

2

Mika’ilu Shu’aibu (Ghari)

SSA

Hisbah

3

Muhktar Abdullahi Shuwaki (Ghari)

SSA

Filaye

4

Engr. Sagir Lawan Waziri (Ghari)

SSA

Harkokin al'umma da tallafi

5

Najeef Abdulsalam

SSA

Yan Akwati (Maza)

6

Huwaila Iguda

SSA

Yan Akwati II (Mata)

7

Naziru Hamidu Bako

SSA

KAROTA

8

Usman Abbas Sunusi

SSA

Mai kula da tsare-tsare na II

9

Engr. Usman Kofar Naisa

SSA

Filin wasanni na Mahaha

10

Danladi Alhassan Mai-Bulala

SSA

Tattaro kan jama'a na II

11

Abdulkhadir Umar Kwankwaso

SSA

Ilimi (Abuja)

12

Balarabe Aminu Yusuf

SSA

Harkokin gida na III (Gidan bakin gwamnati)

13

Shukurana Garba Langel

SSA

Tattaro kan jama'a - Kano ta Arewa

14

Mustapha Ma'aruf Diso

SSA

Kiwon lafiya a matakin farko

15

Garba Yahaya Labour

SSA

Zirga-zirga (I)

16

Humaira Sharif

SSA

Wayar da kan mata

17

Muttaka Sani Gaya

SSA

Kungiyoyin magoya baya na III

18

Gausu Nuhu Wali

SSA

Fasahohin gargajiya

19

Hadiza Sale (Baby)

SSA

Tsaftar muhalli

Kara karanta wannan

Bayan jita jitar zai bar APC, Tinubu ya naɗa tsohon gwamnan Nasarawa muƙami

Gwamna Abba Yusuf ya ce yana fatan wadanda ya nada za su taimaka masa wajen ciyar da Kano gaba
Gwamnan jihar Kano, Mai Girma Abba Kabir Yusuf. Hoto: @Kyusufabba
Source: Twitter

Fatan gwamnati ga sababbin hadimai 19

Gwamnatin jihar Kano ta bayyana kyakkyawan fata cewa sababbin hadiman za su yi amfani da gwanintarsu da kuma kwazonsu wajen ba da gudunmawa ga ci gaban jihar.

Ta bakin Sanusi Dawakin Tofa, Gwamna Abba Yusuf ya ce yana fatan wadanda ya nada za su taimaka masa wajen samawa al'ummar Kano ayyukan more rayuwa.

An sa ran wannan ƙarin hadiman zai ƙara inganta ayyukan gwamnati a sassa daban-daban, tare da bai wa gwamnatin damar isar da ayyukanta ga birane da kauyuka.

Abba ya nada Ahmed Musa manajan Kano Pillars

A wani labarin, mun ruwaito cewa, Gwamna Abba Yusuf ya naɗa Ahmed Musa a matsayin sabon manajan Kano Pillars, tare da kafa sabon kwamitin gudanarwa don farfaɗo da ƙungiyar.

An sake nada yawancin tsofaffin mambobin kwamitin da ya jagoranci ƙungiyar a kakar da ta gabata an sake, tare da ƙarin sababbin fuska domin tunkarar kakar Firimiyar Najeriya (NPL).

Gwamnatin jihar ta bayyana cewa nadin Ahmed Musa, wanda fitaccen ɗan wasa ne a duniya, zai kawo sabon salo, ƙwarewa da ɗaukaka ga ƙungiyar Kano Pillars a matakin ƙasa da ƙasa.

Wanda ya tantance Muhammad Malumfashi, babban edita a Legit.ng.

Asali: Legit.ng

Authors:
Sani Hamza avatar

Sani Hamza (Hausa Editor) Sani Hamza ma'aikaci ne da ya yake da gogewa a aikin jarida. Ba fassara labarai da wallafasu a yanar gizo kadai ba, Sani yana da kwarewa a aikin rediyo da talabijin. Ya kuma shafe shekaru 8 a masana'antar fina-finai da dab'i. Imel: sanihamzafuntua@gmail.com