'Yan Bindiga Sun Yi Ta'asa a Wani Mummunan Hari a Kebbi

'Yan Bindiga Sun Yi Ta'asa a Wani Mummunan Hari a Kebbi

  • An shiga jimami a jihar Kebbi biyo bayan wani mummunan harin ta'addancin da ƴan bindiga suka kai kan mutanen da ba su ji ba, ba su gani ba
  • Ƴan bindigan sun hallaka mutane da dama a yayin harin wanda suka kai a ƙauyen Tadurga da ke ƙaramar hukumar Zuru
  • Tantiran sun kuma yi awon gaba da wasu mutane zuwa cikin daji, tare da sace shanu a harin wanda suka kai cikin dare

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Editan Legit Hausa Sharif Lawal yana da ƙwarewar shekaru wajen kawo rahotannin siyasa, al'amuran yau da kullum, tsegumi da nishaɗi

Jihar Kebbi - Wasu miyagu da ake zargin ƴan bindiga ne sun kai hari a garin Tadurga da ke ƙaramar hukumar Zuru ta jihar Kebbi.

Ƴan bindigan sun kai harin ne a daren ranar Litinin, inda suka kashe mutane da dama waɗanda ba a tabbatar da adadinsu ba, yayin da suka yi garkuwa da wasu kuma suka sace dabbobi.

Kara karanta wannan

Yaki ya barke tsakanin Rasha da Ukraine, makami mai linzami ya kashe mutane 15

'Yan bindiga sun kai hari a Kebbi
'Yan bindiga sun kashe mutane a Kebbi Hoto: @HQNigerianArmy, @NasirIdrisKIG
Source: Facebook

Wani mazaunin garin mai suna Audu Sule ya ya tabbatar da aukuwar lamarin ga tashar Channels tv.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Ƴan bindiga sun yi ɓarna a Kebbi

Audu Sule ya bayyana cewa maharan sun zo garin da yawansu, inda suka riƙa harbi ba kakkautawa tare da haddasa firgici a tsakanin jama’a.

"Sun shigo da yawa, suna harbi a ko’ina, suka ɓalle shaguna suna sace kaya, sannan suka kashe mutane da dama, suka yi garkuwa da wasu, sannan suka sace shanunmu."

- Audu Sule

Wannan hari na baya-bayan nan na iya yin tasiri wajen rusa ci gaban da aka samu a yaki da ƴan bindiga tun bayan da Gwamna Nasir Idris ya hau mulki.

Wani mazaunin yankin, Abdullahi Zuru, ya ce ƙoƙarin da gwamnatin ke ci gaba da yi ya taimaka wajen korar ƴan bindiga daga yankin, lamarin da ya bai wa manoma damar komawa gonakinsu har ma suka samu amfanin gona mai yawa.

Kara karanta wannan

Ana batun sulhu a Katsina, ƴan bindiga sun kashe jami'an tsaro da tulin manoma

"Duk da wannan harin da aka kai kwanan nan, masarautar Zuru na samun zaman lafiya."

- Abdullahi Zuru

'Yan bindiga sun kai harin ta'addanci a Benue
'Yan bindiga sun sace mutane a Kebbi Hoto: Legit.ng
Source: Original

Me ƴan sanda suka ce kan harin?

Legit Hausa ta tuntuɓi mai magana da yawun rundunar ƴan sandan jihar Kebbi, Nafiu Abubakar, domin samun ƙarin bayani kan lamarin.

Nafiu Abubakar ya bayyana cewa zai bincika domin samun cikakkun bayanai kan harin.

"Eh bari na bincika domin samun ƙarin bayani."

- Nafiu Abubakar

Sai dai har zuwa lokacin haɗa wannan rahoton, ba a sake ji daga gare shi ba.

Karanta wasu labaran kan ƴan bindiga

Ƴan bindiga sun kashe jami'an tsaro

A wani labarin kuma, kun ji cewa wasu tantiran ƴan bindiga sun hallaka jami'an tsaro a jihar Katsina.

Ƴan bindigan sun hallaka jami'an tsaron ne a wani hari da suka kai a ƙauyen Marmara da ke cikin ƙaramar hukumar Malumfashi.

Kara karanta wannan

Bayan kulla sulhu, gwamnatin Katsina ta ja kunnen tubabbun 'yan bindiga

Maharan sun kuma yi ajalin tulin manoma waɗanda ba a riga aka bayyana adadinsu ba, a harin da suka kai a ƙauyen.

Wanda ya tantance Muhammad Malumfashi, babban edita a Legit.ng.

Asali: Legit.ng

Authors:
Sharif Lawal avatar

Sharif Lawal (Hausa Editor) Sharif Lawal ma'aikacin jarida ne wanda ya samu gogewa a harkar aikin jarida. Ya yi digirinsa na farko a jami'ar Ahmadu Bello (ABU) da ke Zaria. Ya samu horo daga Reuters kan aikin jarida da tantance labarai. Za a iya tuntubarsa ta Sharif.lawal@corp.legit.ng