Tsufa Ya Zo da Gardama: Dattijo Ɗan Shekara 50 Ya Ɗirka wa Ƴarsa Ciki a Bauchi

Tsufa Ya Zo da Gardama: Dattijo Ɗan Shekara 50 Ya Ɗirka wa Ƴarsa Ciki a Bauchi

  • Wani dattijo dan shekaru 50, Umar Sule, ya shiga hannun ‘yan sanda bisa zargin dirka wa ’yarsa mai shekaru 17 ciki a jihar Bauchi
  • Lamarin ya faru ne a Kurmin Ado, karamar hukumar Ganjuwa, inda wanda ake zargi ya amsa cewa ya yi lalata da 'yarsa babu adadi
  • Jami’an tsaro na ci gaba da bincike yayin da kwamishinan ‘yan sanda ya bayar da umarnin gurfanar da wanda ake zargi a gaban kotu

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Sani Hamza, kwararren edita ne a fannin nishadi, al'amuran yau da kullum da kuma siyasa. Sani yana da shekaru sama da biyar a aikin jarida

Bauchi - Rundunar 'yan sanda ta kama wani dattijo dan shekara 50 mai suna Umar Sule kan zarginsa da dirka wa 'yarsa ciki a Bauchi.

Lamarin ya faru ne a kauyen Kurmin Ado da ke karkashin gundumar Kariya a karamar hukumar Ganjuwa, jihar Bauchi, kamar yadda rundunar 'yan sanda ta tabbatar.

Kara karanta wannan

Rogo ya jawo 'dan shekaru 49 ya sassara mahaifiyarsa da adda har barzahu

'Yan sanda sun yi magana da aka kama mahaifin da ya dirka wa yarsa ciki a Bauchi
Shugaban 'yan sandan Najeriya, Kayode Adeolu Egbetokun. Hoto: @PoliceNG
Asali: Twitter

An cafke dattijo kan lalata da 'yarsa a Bauchi

Kakakin rundunar na Bauchi, CSP Ahmed Wakili, ya bayyana hakan cikin wata sanarwa da ya rabawa menam labarai, inji rahoton Tribune.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

A cewarsa CSP Ahmed Wakili:

“A ranar 3 ga Afrilu, 2025, misalin karfe 4:30 na yamma, rundunar 'yan sandan Bauchi ta samu korafi daga wani mai suna Abdullahi Baban Karatu.
“Wanda ya kai korafin dan Kurmin Ado ne, kuma ya zargi wani mai suna Umar Sule, mai shekaru 50, da aikata wannan mummunan laifi.”

Jaridar Punch ta rahoto ASP Wakili ya kara da cewa:

“An ce a watan Nuwambar shekarar 2024, Umar ya yi lalata da 'yarsa a dakin matarsa a lokuta daban-daban cikin dare.”

Bauchi: Yadda mahaifi ya dirka wa 'yarsa ciki

Bayan karɓar wannan rahoto, rundunar ta tura wata tawaga ta kwararrun jami’ai domin bincike da kuma kama wanda ake zargi da aikata laifin.

A yayin binciken, wanda ake zargin ya amsa laifinsa a fili, yana mai cewa ya sadu da 'yarsa ba sau daya ko biyu ba, har ta samu ciki.

Kara karanta wannan

Portable: Ƴan sanda sun kama fitaccen mawakin Najeriya, an ji laifin da ya aikata

A cewar rahoton wani kwararren likita, an tabbatar cewa yarinyar tana dauke da juna biyu na wata uku sakamakon cin zarafin da mahaifinta ya yi.

A yayin hira da yarinyar, ta tabbatar da cewa mahaifinta ne ke lalata da ita, kuma hakan ya faru ne lokacin da mahaifiyarta ba ta gari, ta yi tafiya.

Ta ce mahaifiyarta ta je ziyara wurin iyayenta a kauyen Burra, karamar hukumar Ningi, lokacin da mahaifinta ya fara amfani da damar yana lalata da ita.

'Yan sanda za su gurfanar da dattijo gaban kotu

'Yan sanda za su gurfanar da mahaifin da ya dirka wa 'yarsa ciki a Bauchi
Taswirar jihar Bauchi. Hoto: Legit.ng
Asali: Original

Bayan dawowar mahaifiyarta daga tafiya, ta lura da canjin yanayi a jikin yarinyar, inda ta yi mata tambayoyi, har dai daga bisani ta fada mata cewa mahaifinta ne ya yi mata cikin.

Rundunar ‘yan sanda ta bayyana cewa tana ci gaba da bincike, kuma za a mika lamarin zuwa kotu da zarar an kammala binciken.

Sanarwar ta ce kwamishinan ‘yan sandan Bauchi, CP Sani-Omolori Aliyu, ya bayar da umarni cewa a gurfanar da wanda ake zargi a kotu bayan kammala bincike.

Kara karanta wannan

Yadda darektan APC ya yi wani irin mutuwa a hannun ƴan bindiga a Abuja

An kama wanda ya yi wa yarsa ciki a Adamawa

A wani labarin, mun ruwaito cewa, rundunar ƴan sandan Adamawa ta kama wani magidanci da ake zargi da lalata da ƴar cikinsa har ta samu juna biyu.

'Yan sanda sun ce wanda ake zargin, Matthew Joseph ya fara lalata da yarsa ne bayan ya saki mahaifiyarta kimanin shekara guda.

Binciken da rundunar ta gudanar ya nuna wacce abin ya faru da ita tana dauke da juna biyu na watanni uku kamar yadda likitocin da suka duba ta suka tabbatar.

Asali: Legit.ng

Authors:
Sani Hamza avatar

Sani Hamza (Hausa Editor) Sani Hamza ma'aikaci ne da ya yake da gogewa a aikin jarida. Ba fassara labarai da wallafasu a yanar gizo kadai ba, Sani yana da kwarewa a aikin rediyo da talabijin. Ya kuma shafe shekaru 8 a masana'antar fina-finai da dab'i.