'Yan Bindiga Sun Kai Hari a Daren Juma'a, Mutanen Gari Sun Masu Tara Tara, An Rasa Rai

'Yan Bindiga Sun Kai Hari a Daren Juma'a, Mutanen Gari Sun Masu Tara Tara, An Rasa Rai

  • Ƴan ta'addan Lakurawa sun kai farmaki garin Gulma da ke ƙaramar hukumar Argungu a jihar Kebbi, sun kashe mutum
  • Rahotanni sun nuna cewa ƴan ta'addan sun yi takansu yayin da suka ga mutanen gari sun haɗu, sun fito da niyyar kare kansu
  • Rundunar ƴan sandan jihar ta tabbatar da faruwar lamarin, ta tura dakaru domin kare dukiyoyi da rayukan mazauna garin

Ahmad Yusuf, kwararren edita ne a Legit Hausa da ya shafe tsawon shekaru yana kawo muku rahotannin siyasa, nishadi da al'amuran yau da kullum

Jihar Kebbi - An shiga fargaba a karamar hukumar Argungu ta jihar Kebbi bayan wani hari da ‘yan ta’adda suka kai a garin Gulma a daren Juma'a.

Ƴan ta'addan waɗanda ake kyautata zaton mayakan Lakurawa ne sun afkawa mutanen garin Gulma ne da misalin karfe 11:00 na dare a ranar Alhamis.

Taswirar jihar Kebbi.
Yan ta'addan Lakurawa sun sake kai hari, sun sace mutane a jihar Kebbi Hoto: Legit.ng
Asali: Original

A cewar shugaban ƙaramar hukumar Argungu, Aliyu Sani Gulma, mutum daya ya rasa ransa, yayin da wasu shida suka jikkata a harin, rahoton Daily Trust.

Kara karanta wannan

'Yan bindiga sun kai farmaki masallaci, sun sace limami da masallata

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Mutanen gari sun yi ƙoƙarin kare kansu

Ya ce miyagun ƴan ta'addan sun shiga garin a daidai lokacin da galibin mutane sun shiga gida sun kwanta barci kafin wayewar garin Juma'a.

"‘Yan ta’addan sun shigo garin yayin da mutanen ke barci. Sun kashe mutum daya sannan suka harbi wasu shida, yanzu haka an kwantar da su a Asibitin Tarayya da ke Birnin Kebbi,”

- in ji shi.

Ya kara da cewa ‘yan ta’addan sun ji tsoro, sun tsere zuwa daji da mutanen gari suƙa cire tsoro sannan suka taru suka tunkari maharan gadan-gadan.

"Mun sanar da hukumomin tsaro game da harin, kuma dakarun soji sun isa garin domin kare rayuka da dukiyoyin al'umma," in ji ciyaman.

Yadda ‘yan sanda suka ɗauki mataki

Jami'in hulɗa da jama'a na rundunar ‘yan sandan Kebbi, CSP Nafi’u Abubakar, ya tabbatar da aukuwar lamarin.

Ya ce rundunar ta tura jami’an ‘yan sanda na musamman zuwa yankin domin tabbatar da tsaron mutane.

Kara karanta wannan

Yadda 'yan bindiga sama da 100 suka taru wajen sace Janar Tsiga a Katsina

Sanata Aliero ya ce an fatattaki Lakurawa

Wannan harin ya zo ne bayan tsohon gwamnan Kebbi kuma Sanatan Kebbi ta Tsakiya, Adamu Aliero, ya bayyana cewa sojoji sun fatattaki kungiyar Lakurawa zuwa Jamhuriyar Nijar.

A cewarsa, hakan ya biyo bayan matakan ministan tsaro, Abubakar Badaru, da babban hafsan tsaro da sauran masu ruwa da tsaki suka ɗauka na murƙushe su.

Sanata Aliero ya yi gargadi cewa idan ba a dauki matakin gaggawa ba, yankin Arewa maso Yamma na iya fuskantar irin barnar da ta auku a Arewa maso Gabas.

"Yankin Arewa maso Yamma yana da yawan jama’a, filayen noma da kuma albarkatun ruwa. Saboda haka, dole ne a tabbatar da tsaron yankin kafin al’amura su tabarbare," in ji shi.

Sai dai bayan wannan harin na daren Juma'a, jami'an tsaro sun kai ɗauki garin Gulma kuma ana sa ran matakan da suka ɗauka zai kare aukuwar wani hari a gaba.

Kara karanta wannan

Mummunar gobara ta tashi a makarantar allo, an samu asarar rayukan dalibai

Sojoji sun murƙushe ƴan bindiga 20

A wani rahoton, kun ji cewa dakarun sojojin Najeriya sun yi nasarar hallaka ƴan bindiga sama da 20 a jihohin Kebbi da Sakkwato.

Sojojin sun samu wannan nasara ne yayin ɗa suka kai samame maɓoyar ƴan ta'addan, sun kuma ƙona sansanoninsu.

Muhammad Malumfashi, babban edita a sashen Hausa na Legit ya duba labarin.

Asali: Legit.ng

Authors:
Ahmad Yusuf avatar

Ahmad Yusuf (Hausa editor) Ahmad Yusuf ma'aikacin jaridar Legit.ng sashin Hausa ya fara aiki a 2021, ya kware wajen kawo labarai da rahotanni da suka shafi siyasa da al'amuran yau da kullum. Matashin ɗan jaridar ya koyi Lissafi a digirinsa na farko a Jami'ar Kimiyya da Fasaha da ke Wudil, Kano (KUST) ya kuma samu shaidar kwarewa a fannin aikin jaridar zamani daga Reuters a 2022. Kafin fara aiki da Legit Ahmad ya yi aiki da jaridu da dama na turanci da Hausa tun 2012. Mail: ahmad.yusuf@corp.legit.ng 07032379262