Rana Ta 6: Yadda Zanga Zangar Nuna Kin Jinin Gwamnatin Tinubu Ke Gudana a Jihohin Najeriya

All posts
Key Events
Analysis
Exclusive
9 Posts
Sort by
Our live updates have concluded for the day. Catch up on everything you missed below.
Muhammad Malumfashi avatar Salisu Ibrahim avatar Sharif Lawal avatar
daga Muhammad Malumfashi, Salisu Ibrahim, Sharif Lawal, Aisha Ahmad and Ibrahim Yusuf

Sojoji sun kashe wani yaro a Zariya

A unguwar Samaru da ke Zariya, Legit ta samu labarin jami’an tsaro sun hallaka wani yaro mai shekara 16 da haihuwa.

Legit ta samu labari cewa sojoji sun harba bindiga, harsashi ya shigo kofar gida har ya kashe Ismail Ahmad dazu da safe.

Abin ya faru ne da kimanin karfe 11:00 na safiyar Talata a layin Sarkin Pawa da ke Hayin Dogo.

A shafinsa na Facebook, wani Khalifa Ringim II ya wallafa hotunan gawar wannan yaro da ake shirin birnewa a halin yanzu.

Muhammad Malumfashi avatar Salisu Ibrahim avatar Sharif Lawal avatar
daga Muhammad Malumfashi, Salisu Ibrahim, Sharif Lawal, Aisha Ahmad and Ibrahim Yusuf

An watsar da zanga-zanga a garuruwa

Rahotanni daga tashar Channels sun tabbatar da cewa an yi watsi da zanga-zangar da ake yi da aka duba tituna a safiyar ranar Talata

Daga cikin dalilan akwai dokar hana fita da aka rika kakabawa a garuruwa dabam-dabam a Najeriya saboda yadda lamarin ya cabe.

Muhammad Malumfashi avatar Salisu Ibrahim avatar Sharif Lawal avatar
daga Muhammad Malumfashi, Salisu Ibrahim, Sharif Lawal, Aisha Ahmad and Ibrahim Yusuf

An yi fashe-fashe a Zariya

Legit Hausa ta samu labari dazu cewa ya canza a garin Zariya inda aka yi zanga-zanga cikin kwanciyar hankali a makon da ya gabata.

Bata-gari sun fasa shagunan ‘yan kasuwa a unguwar PZ da ke karamar hukumar Sabon Gari a Kaduna safiyar Litinin 5 ga watan Agusta.

Jami’an ‘yan sanda sun yi kokari wajen ganin lamarin ya lafa inda aka watsa borkonon tsohuwa kuma aka cafke wasu miyagun matasan.

Majiyoyi sun shaida mana cewa wadannan matasa sun nufi wata unguwar bayan barin PZ.

Muhammad Malumfashi avatar Salisu Ibrahim avatar Sharif Lawal avatar
daga Muhammad Malumfashi, Salisu Ibrahim, Sharif Lawal, Aisha Ahmad and Ibrahim Yusuf

Zanga Zanga: Yan Sanda Su Tarwatsa Masu Ɗauke da Tutar Rasha

Zanga zanga ta barke a jihar Katsina yayin da al'umma da dama suka fito dauke da tutocin kasar Rasha suna ihun cewa yunwa za ta kashe su.

Sai dai Jaridar Daily Trust ta wallafa cewa rundunar yan sanda ta tarwatsa matasan ta hanyar fesa musu borkonon tsohuwa.

Matasa sun fito zanga zanga a Katsina ne bayan kwana uku ba su fito kan tituna ba kuma ana ganin kalaman shugaban kasa na ranar Lahadi ne suka fusatasu.

Muhammad Malumfashi avatar Salisu Ibrahim avatar Sharif Lawal avatar
daga Muhammad Malumfashi, Salisu Ibrahim, Sharif Lawal, Aisha Ahmad and Ibrahim Yusuf

Jami'an tsaro sun cafke masu zanga-zanga a Abuja

Jami'an tsaro sun tarwatsa masu zanga-zanga a yankin Karu da ke birnin tarayya Abuja.

Jaridar The Punch ta ce masu zanga-zangar sun fara taruwa ne lokacin da jami'an tsaro suka rufar musu inda suka cafke mutum uku.

Muhammad Malumfashi avatar Salisu Ibrahim avatar Sharif Lawal avatar
daga Muhammad Malumfashi, Salisu Ibrahim, Sharif Lawal, Aisha Ahmad and Ibrahim Yusuf

Masu zanga-zanga sun fito a Legas

Wasu daga cikin masu zanga-zanga sun fito a Legas domin ci gaba da nuna adawa da halin yunwa da tsadar rayuwar da ake fama da ita a ƙasar nan.

Jaridar Daily Trust ta sanya bidiyon masu zanga-zangar a shafinta na X.

Muhammad Malumfashi avatar Salisu Ibrahim avatar Sharif Lawal avatar
daga Muhammad Malumfashi, Salisu Ibrahim, Sharif Lawal, Aisha Ahmad and Ibrahim Yusuf

An tsaurara matakan tsaro a Legas

An jibge jami'an tsaro masu yawa a dandalin Gani Fawehinmi da ke Ojota a jihar Legas.

Jaridar Premium Times ta ce kwamishinan ƴan sandan jihar Legas, Adegoke Fayoade na daga cikin jami'an tsaron da ke wajen.

Muhammad Malumfashi avatar Salisu Ibrahim avatar Sharif Lawal avatar
daga Muhammad Malumfashi, Salisu Ibrahim, Sharif Lawal, Aisha Ahmad and Ibrahim Yusuf

An sanya dokar hana fita a Plateau

Gwamnatin jihar Plateau ta sanya dokar hana fita ta sa'o'i 24 a birnin Jos da Bukuru.

Jaridar Leadership ta ce an sanya dokar ne biyo bayan wasu ɓata gari da suka ɓalle shaguna tare da sace dukiyoyi a birnin na Jos yayin zanga-zangar da ake gudanarwa.

Muhammad Malumfashi avatar Salisu Ibrahim avatar Sharif Lawal avatar
daga Muhammad Malumfashi, Salisu Ibrahim, Sharif Lawal, Aisha Ahmad and Ibrahim Yusuf

Masu shirya zanga-zanga za su yi jawabi

Masu shirya zanga-zangar #Endbadgovernance a Najeriya za su yi taron manema labarai a ranar Litinin, 5 ga watan Agustan 2024.

Za a gudanar da taron ne a dandanlin Gani Fawehinmi Freedom Park da ke Ojota a jihar Legas.

Tsohon ɗan takarar shugaban ƙasa, Omoyele Sowore ne ya bayyana hakan a shafinsa na X da safiyar ranar Litinin.