Yan Bindiga Sun Gwabza Fada, Hatsabibin Mai Garkuwa da Mutane Ya Sheka Lahira
- Rundunar sojin Najeriya ta kai farmaki kan yan bindiga a wasu ƙananan hukumomin jihar Taraba a Arewa maso gabas
- Wani gawurtaccen mai garkuwa da mutane ya sheka lahira a karamar hukumar Wukari bayan sun yi fada a tsakaninsu
- Haka zalika rundunar sojin ta yi nasarar ƙubutar da wasu mata da yan bindiga suka yi garkuwa da su a garin Lau
Editan Legit Hausa Ibrahim Yusuf yana da gogewar aikin jarida da rubuce-rubucen adabi sama da shekaru hudu, kuma kwararre ne a kawo rahotannin kasuwanci, siyasa da lamuran yau da kullum.
Jihar Taraba - Dakarun sojin Najeriya sun kai jerin hare haren kan yan bindiga a wasu yankunan jihar Taraba.
Rundunar sojin ta samu nasarar ƙubutar da wadanda aka sace da kama wasu masu garkuwa da mutane.

Asali: Facebook
Wani mai garkuwa da mutane ya sheka lahira yayin da fada ya kaure a tsakaninsu kamar yadda rundunar sojin ta wallafa a shafin Facebook.
LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng
Fada ya kaure tsakanin yan bindiga
Bayan jin karar harbe harbe a yankin Chinkai a garin Wukari, rundunar sojin Najeriya ta yi gaggawar isa wajen.
Da zuwan sojojin suka samu yan bindiga ne suka yi mummunan fada a tsakaninsu kuma sun samu wani dan bindiga mai suna Alhaji Gana kwance cikin jini.
Alhaji Gana yana cikin miyagun yan bindiga da ake nema ruwa a jallo kuma ya fitini jihar Taraba da ayyukan barna.
Sojoji sun ceto mutane a Lau
A ranar 8 ga watan Yuli sojojin Najeriya suka kai farmaki kan maboyar yan bindiga a dutsen Adamu Katibu a karamar hukumar Lau.
Farmakin ya jawo nasarar kama masu garkuwa da mutane uku da ceto wasu mata biyu da suka kama.
A ranar 7 ga watan Yuli yan bindigar suka sace matan, Asma'u da Hauwa'u kuma an mika su ga iyalansu bayan duba lafiyarsu a asibiti.
Yan bindiga sun yi fada a Zamfara
A wani rahoton, kun ji cewa an gwaba ƙazamin faɗa a tsakanin ƙungiyoyin ƴan bindiga uku a jihar Zamfara wanda ya jawo aka samu asarar rayuka masu yawa.
A mummunan artabun dai an hallaka shugabannin ƴan bindiga biyu, Kachallah Gwande da Ƙachallah Madagwal tare da mayaƙa mutum 12.
Asali: Legit.ng