Yan Bindiga Sun Gwabza Fada, Hatsabibin Mai Garkuwa da Mutane Ya Sheka Lahira

Yan Bindiga Sun Gwabza Fada, Hatsabibin Mai Garkuwa da Mutane Ya Sheka Lahira

  • Rundunar sojin Najeriya ta kai farmaki kan yan bindiga a wasu ƙananan hukumomin jihar Taraba a Arewa maso gabas
  • Wani gawurtaccen mai garkuwa da mutane ya sheka lahira a karamar hukumar Wukari bayan sun yi fada a tsakaninsu
  • Haka zalika rundunar sojin ta yi nasarar ƙubutar da wasu mata da yan bindiga suka yi garkuwa da su a garin Lau

Editan Legit Hausa Ibrahim Yusuf yana da gogewar aikin jarida da rubuce-rubucen adabi sama da shekaru hudu, kuma kwararre ne a kawo rahotannin kasuwanci, siyasa da lamuran yau da kullum.

Jihar Taraba - Dakarun sojin Najeriya sun kai jerin hare haren kan yan bindiga a wasu yankunan jihar Taraba.

Rundunar sojin ta samu nasarar ƙubutar da wadanda aka sace da kama wasu masu garkuwa da mutane.

Kara karanta wannan

Sojoji sun ragargaji 'yan ta'adda a jihohi, sun kwato makamai da dama

Sojojin Najeriya
Sojoji sun ceto mata a Taraba. Hoto: HQ Nigerian Army.
Asali: Facebook

Wani mai garkuwa da mutane ya sheka lahira yayin da fada ya kaure a tsakaninsu kamar yadda rundunar sojin ta wallafa a shafin Facebook.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Fada ya kaure tsakanin yan bindiga

Bayan jin karar harbe harbe a yankin Chinkai a garin Wukari, rundunar sojin Najeriya ta yi gaggawar isa wajen.

Da zuwan sojojin suka samu yan bindiga ne suka yi mummunan fada a tsakaninsu kuma sun samu wani dan bindiga mai suna Alhaji Gana kwance cikin jini.

Alhaji Gana yana cikin miyagun yan bindiga da ake nema ruwa a jallo kuma ya fitini jihar Taraba da ayyukan barna.

Sojoji sun ceto mutane a Lau

A ranar 8 ga watan Yuli sojojin Najeriya suka kai farmaki kan maboyar yan bindiga a dutsen Adamu Katibu a karamar hukumar Lau.

Farmakin ya jawo nasarar kama masu garkuwa da mutane uku da ceto wasu mata biyu da suka kama.

Kara karanta wannan

Cikakkun sunaye da bayanan jihohi 7 da ake son kirkira a Najeriya

A ranar 7 ga watan Yuli yan bindigar suka sace matan, Asma'u da Hauwa'u kuma an mika su ga iyalansu bayan duba lafiyarsu a asibiti.

Yan bindiga sun yi fada a Zamfara

A wani rahoton, kun ji cewa an gwaba ƙazamin faɗa a tsakanin ƙungiyoyin ƴan bindiga uku a jihar Zamfara wanda ya jawo aka samu asarar rayuka masu yawa.

A mummunan artabun dai an hallaka shugabannin ƴan bindiga biyu, Kachallah Gwande da Ƙachallah Madagwal tare da mayaƙa mutum 12.

Asali: Legit.ng

Authors:
Ibrahim Yusuf avatar

Ibrahim Yusuf (Hausa Editor) Ibrahim Yusuf yana da gogewar aikin jarida da rubuce-rubucen adabi sama da shekaru hudu, kuma kwararre ne a kawo rahotannin kasuwanci, siyasa da lamuran yau da kullum. ibrahim.yusuf@corp.legit.ng