Abubuwa 10 da Suka Faru da Sanusi II Tun da Ya Koma Karaga a Tsakiyar Rikicin Sarauta

Abubuwa 10 da Suka Faru da Sanusi II Tun da Ya Koma Karaga a Tsakiyar Rikicin Sarauta

Kano - Abubuwa da-dama sun faru da Muhammadu Sanusi II daga lokacin da aka maido da shi kan karagar mulki zuwa yau.

M. Malumfashi ya shafe shekaru ya na kawo labaran Hausa musamman na siyasa, addini, tarihi, wasanni da al’ada.

A wannan rahoto, Legit ta shiga masarautar ta Kano mai dinbin tarihi domin tattaro abubuwan da aka yi cikin wata guda.

Sarki Sanusi
Gwamnan Kano tare da Sarki Muhammadu Sanusi II Hoto: Abba Kabir Yusuf
Asali: Twitter

1. Sanar da nadin Muhammadu Sanusi II

A ranar Alhamis, 23 ga watan Mayu 2024, Abba Kabir Yusuf ya sanar da cewa Muhammadu Sanusi II ya dawo mulki.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Abba Yusuf ya dauki matakin bayan sa hannu a dokar masarauta ta shekarar 2024. Daily Trust ta kawo wannan labari lokacin.

2. Mikawa Sarki Sanusi II takarda

Kara karanta wannan

‘Burgar banza’: Hadimin Ganduje ya takalo Abba kan yunkurin fatattakar Sarki Aminu

Washegari sai gwamna Abba Kabir Yusuf ya mikawa Khalifa Muhammadu Sanusi II takardar nadi a matsayin Sarkin Kano.

3. Shiga fadar Sarkin Kano

Bayan awanni sai manyan jami’an gwamnatin Kano su ka yiwa Mai martaba Malam Muhammadu Sanusi II rakiya zuwa fada.

A wannan lokaci Alhaji Aminu Ado Bayero yana kan hanyar dawowa daga tafiya da ya yi.

4. Sanusi ya yi limancin sallar Juma’a

Khalifan na darikar Tijjaniya kuma Martaba Sarki ne ya jagoranci sallar Juma’ar farko da ya yi a masallacin Sarki da ke Kofar Kudu.

A hudubar da ya gabatar, an ji Sarki ya yi maganar muhimmancin imani da kaddara.

5. Umarni dabam-dabam daga kotu

Daga nan kotu suka rika ba da umarni mabanbanta kan rikicin masarautar. Mai shari’a Aisha Adamu Aliyu ta ce a kori Aminu Bayero.

Can kuma sai aka ji kotun tarayya ta ba da hukuncin korar Sarkin Kano daga cikin fadar kamar yadda Leadership ta tattaro labarin.

Kara karanta wannan

Hadimin Buhari ya ja kunnen Abba kan yunkurin ruguza fadar Aminu a Nassarawa

6. Sarki Sanusi II ya karbi mubaya’a a Kano

Bayan abubuwa sun soma lafawa, Sarki Sanusi II ya fara karbar gaisuwa daga talakawa da kuma mubaya’a daga wajen hakiman Kano.

Mafi yawan hakimai sun yi mubaya’a ga sabon sarkin da aka dawo da shi a nan ne kuma aka samu sabani daga gidan Sheikh Dahiru Bauchi.

7. Fito da fai-fen murya

Ana haka sai ga wani fai-fai yana yawo inda wasu suka yi ikirarin Mai martaba ne yake waya da wani kafin dawo da shi kan karaga.

Masoya sun ce kirkirar sautin aka yi da fasahar zamani ko akalla kwaikwayon muryar.

8. Wasika daga dangin Inyass

Ba a gama wannan ba kuma sai ga wata wasika da aka yi ikirari ta fito ta hannun Sheikh Mahe Niasse a madadin gidan Ibrahim Inyass.

Wannan wasika da daga baya aka gano ta karya ce, ta yi kira ga Sarki ya hakura da sarauta, ya yi koyi da kakansa Muhammadu Sanusi II.

Kara karanta wannan

Kano: Yadda Sanusi II da Aminu Bayero suka yi Sallar Jumu'a bayan hukuncin kotu

9. Shirin hawa sallah a Kano

Ana shirye-shiryen bikin idi ne kuma sai ‘yan sanda suka fitar da sanarwar haramta hawa sallah. Hakan ya takawa har Aminu Ado Bayero burki.

10. Hukuncin kotu kan rikicin sarauta

Kotun tarayya ta zartar da hukuncin da ya bata dukkan matakan da Abba Kabir ya dauka bayan ya rattaba hannu a sabuwar dokar masarauta.

Sanusi II ne Sarki ko Aminu?

Bayan hukuncin kotu, amsa ta fito a kan wanene sahihin Sarkin Kano ta fuskar doka kamar yadda aka ji labari Abba Hikima ya fayyace batun.

Barista Abba Hikima ya ce har gobe Alhaji Aminu Ado Bayero yana kan karagar mulki domin alkali ya dakatar da aiki da sabuwar doka.

Asali: Legit.ng

Authors:
Muhammad Malumfashi avatar

Muhammad Malumfashi (Hausa writer) M. Malumfashi ya samu Digirin farko a ilmin komfuta a ABU Zaria. Baya ga haka ya yi Digirgir a fannin kula da bayanai da wani Digirgir a ilmin aikin jarida duk daga jami'ar. Malumfashi ya kan kawo labaran siyasa, addini, wasanni da al’ada. Ya halarci taron karawa juna sani iri-iri. Imel: muhammad.malumfashi@corp.legit.ng

Online view pixel