Kano: Dan Majalisar Yanki Ya Yi Wa Marayu 120 Gata, Za Su Fara Zuwa Makaranta

Kano: Dan Majalisar Yanki Ya Yi Wa Marayu 120 Gata, Za Su Fara Zuwa Makaranta

  • Akalla marayu 120 ne wani kansila a karamar hukumar Wudil ta jihar Kano, Bashir Aliyu, ya dauki nauyin karatun su
  • Kamar yadda ya bayyana yayin kaddamar da rabon kayayyakin karatu ga yaran, Hon Aliyu ya ce tallafin zai gyara goben marayun
  • Kansilan ya jaddada cewa zai dauki nauyin karatun wadanda suka ci gajiyar tallafin tun daga karama har zuwa babbar sakandire

Sani Hamza, kwararren edita ne a fannin nishadi, al'amuran yau da kullum da kuma siyasa. Sani yana da shekaru sama da biyar a aikin jarida

Jihar Kano - Kansila mai wakiltar gundumar Achika ta karamar hukumar Wudil a jihar Kano, Bashir Aliyu, ya dauki nauyin karatun yara marayu 120 da aka kora daga makaranta.

An dauki nauyin karatun marayu a Kano
Kano: Kansila ya dauki nauyin karatun marayu 120. Hoto: Hildi Photography
Asali: UGC

A wani bikin bayar da kayayyakin karatu ga yaran da aka gudanar a gundumar Achika a ranar Lahadi, Hon. Aliyu ya ce ya yi hakan domin gyara makomar marayun.

Kara karanta wannan

Kudurin ƙirƙirar sabuwar jiha a Kudu maso Gabas ya wuce karatun na 1 a majalisar wakilai

Kansila ya dauki nauyin karatun marayu

Hon. Aliyu ya ce za a yi wa yaran rajista a karamar sakandare ta gwamnati da ke Achika da kuma karamar sakandaren Arabiyya ta Achika, in ji rahoton Daily Nigerian.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Ya kara da cewa zai dauki nauyin karatun wadanda suka ci gajiyar tallafin tun daga karama har zuwa babbar sakandire ko da kuwa ba ya rike da wani mukamin siyasa.

Kansilan ya yi nuni da cewa, hakan shi ne irin gudunmawar da zai bayar wajen ci gaban jihar Kano wadda za ta karfafa wa marayu da marasa galihu.

An raba kayan karatu ga daliban

Ya bayyana cewa ya fito da wannan shiri ne a wani yunkuri na tabbatar da makomar yara musamman marayu da a halin yanzu ke samun koma baya wajen yin karatu.

Kara karanta wannan

NLC na neman ƙarin albashi, Tinubu ya bayyana wani muhimmin aiki da zai yi zuwa 2030

Hon. Aliyu ya bayyana cewa daga cikin wadanda suka ci gajiyar tallafin, 65 mata ne yayin da 54 kuma maza ne.

Kayayyakin da aka raba wa wadanda suka ci gajiyar tallafin sun hada da littattafan rubutu guda 1,200, jakunkunan makaranta 120, saiti 240 na kayan makaranta da kuma saiti 240 na takalma.

Abba ya biya wa dalibai kudin NECO

A wani labarin, mun ruwaito cewa gwamnan jihar Kano, Abba Yusuf ya biya wa dalibai 119,903 kudin jarabawar NECO da NBAIS ta 2024.

Gwamna Abba Kabir Yusuf na jihar Kano ya amince a fitar da Naira biliyan 2.9 domin biyan kudin jarabawar ne ga daliban da suka samu makin 'C' a darusa 5 na jarabawar 'Mock.'

Asali: Legit.ng

Authors:
Sani Hamza avatar

Sani Hamza Sani Hamza ma'aikaci ne da ya yake da gogewa a aikin jarida. Ba fassara labarai da wallafasu a yanar gizo kadai ba, Sani yana da kwarewa a aikin rediyo da talabijin. Ya kuma shafe shekaru 8 a masana'antar fina-finai da dab'i.

Online view pixel