InnalilLahi: Tsohon Shugaban Hukumar EFCC, Lamorde Ya Rasu Yana da Shekaru 61
- An shiga jimami bayan rasuwar tsohon shugaban hukumar EFCC, Ibrahim Lamorde a Masar bayan fama da jinya mai tsayi
- Marigayin kafin rasuwarsa ya rike shugabancin hukumar EFCC a zamanin mulkin tsohon shugaban kasa, Goodluck Jonathan
- Daga bisani Muhammadu Buhari ya sallame shi bayan ɗarewa karagar mulki a watan Nuwambar 2015 da maye gurbinsa da Ibrahim Magu
Abdullahi Abubakar, Editan Legit Hausa ne a bangaren siyasa, kasuwanci da al'amuran yau da kullum ne, ya na da gogewar aikin jarida sama da shekaru uku.
Jihar Adamawa - Tsohon shugaban hukumar EFCC, Ibrahim Lamorde ya riga mu gidan gaskiya yana da shekara 61.
Marigayin ya rasu ne a kasar Masar yayin da ya je domin yin jinya kamar yadda aka sanar da safiyar yau Lahadi 26 ga watan Mayu.

Asali: Twitter
Lokacin da Lamorde ya rike shugabancin EFCC
Premium Times ta tattaro cewa kafin rasuwar Lamorde, ya rike shugabancin hukumar EFCC daga shekarar 2011 zuwa 2015.
LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng
Lamorde ya rasu da misalin karfe 3:00 na dare bayan an yi masa tiyata kwanaki uku da suka wuce.
An haifi Lamorde a ranar 20 ga watan Disambar shekarar 1962 a jihar Adamawa inda ya shiga aikin dan sanda a shekarar 1986.
An nada Lamorde a matsayin shugaban rikon kwarya na hukumar a watan Nuwambar 2011 a mulkin Goodluck Jonathan, cewar TheCable.
Lamorde ya zama shugaban hukumar EFCC
Daga bisani an tabbatar da Lamorde a matsayin shugaban hukumar a watan Faburairun 2012 har zuwa 9 ga watan Nuwambar 2015.
Bayan tsohon shugaban kasa, Muhammadu Buhari ya yi nasarar lashe zabe a 2015, ya cire Lamorde tare da sauya shi da Ibrahim Magu a matsayin shugaban rikon kwarya na hukumar.
Tun farko, an nada Lamorde daraktan ɓangaren ayyuka na EFCC lokacin da aka kirkiri hukumar a shekarar 2003.
Kanin Uba Sani ya rasu a Kaduna
A wani labarin, kun ji cewa Gwamna Uba Sani na jihar Kaduna ya sanar da rasuwar kaninsa a ranar Juma'a 24 ga watan Mayu.
Uba Sani ya nuna alhini rasuwar Mukhtar Lawal Isma'il wanda ya kwatanta a matsayin mutun mai ƙan-ƙan da kai da kuma himma a ayyukansa.
A karshe, ya yi addu'ar samun rahama ga marigayin da kuma hakurin jure rashin da suka yi a matsayin ƴan uwansa da masoyansa.
Asali: Legit.ng