Ondo: Jam'iyyar APC Ta Ayyana Zaben Fidda Gwanin Jihar 'Inconclusive', Ta Fadi Dalilai

Ondo: Jam'iyyar APC Ta Ayyana Zaben Fidda Gwanin Jihar 'Inconclusive', Ta Fadi Dalilai

Yayin da ake gudanar da zaben fidda gwani a jihar Ondo, jam'iyyar APC ta ayyana zaben wanda bai kammala ba

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Abdullahi Abubakar, Editan Legit Hausa ne a bangaren siyasa, kasuwanci da al'amuran yau da kullum ne, ya na da gogewar aikin jarida sama da shekaru uku.

Jihar Ondo - Jam'iyyar APC ta ayyana zaben fidda gwanin jihar Ondo wanda bai kammala ba.

Jam'iyyar ta dauki matakin ne bayan samun rahotanni daga unguwanni 203 da kuma kananan hukumomi 18.

APC ya ayyana zaben fidda gwanin jam'iyyar wanda bai kammala ba
Jam'iyyar APC ta ce zaben fidda gwani a Ondo bai kammala ba. Hoto: Olusola Oke, Lucky Aiyedatiwa, Jimoh Ibrahim.
Asali: Facebook

Wane mataki APC ta dauka kan zaben?

Shugaban kwamitin zaben fidda gwanin, Gwamna Usman Ododo na jihar Kogi shi ya tabbatar da haka, cewar rahoton AIT.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Ododo ya ce zaben bai gudana ba a wasu ƙananan hukumomi saboda rashin kawo kayan zaben da kuma masu gudanarwa saboda wasu matsaloli.

Kara karanta wannan

Abin da ba a taba yi ba: Dan Najeriya ya kafa tarihi a duniyar wasan 'Chess', Tinubu ya yaba masa

Ya ce za a gudanar da zaben fidda gwanin a unguwannni 13 da ke karamar hukumar Okitipupa da misalin karfe 12:00 na a yau Lahadi 21 ga watan Afrilu.

Yankin na dauke da mambobin da suka yi rijista da suka kai akalla 9,515 wadanda za su gudanar da zaben a karamar hukumar, cewar Premium Times.

A jiya ne wasu miyagu suka tarwatsa zaben fidda gwanin da ake yi a Ward 1 da ke karamar hukumar inda suka lalata komai.

Fasto ya yi hasashen zaben Ondo

Har ila yau, Shugaban cocin Evangelical Spiritual, Fasto Elijah Ayodele ya yi hasashen abin da zai faru a zaben jihohin Edo da Ondo.

Faston ya yi hasashen ne bayan wakilin jaridar Punch ya yi masa tambaya a wata tattaunawa da suka yi.

Wannan hasashe na zuwa ne bayan hukumar INEC ta sanya watan Satumba domin zaben jihar Edo yayin da za a yi na jihar Ondo a Nuwamba.

Kara karanta wannan

Ondo: Rigima ta barke yayin zaben fidda gwanin jami'yyar APC, an lalata komai

Tsagin APC ya dakatar da Ganduje

A wani labarin, kun ji cewa, an samu sabuwar takaddama yayin da tsagin jam'iyyar APC a matakin unguwa ya sake dakatar da Abdullahi Ganduje a jami'yyar.

Jam'iyyar ta dauki matakin ne bayan wani tsagin jam'iyyar a Ganduje da ke karamar hukumar Dawakin Tofa ya musanta dakatar da Ganduje.

Sakataren jam'iyyar a gundumar Ganduje, Ja'afar Adamu Ganduje shi ya tabbatar da haka inda ya ce suna zargin Ganduje da wasu zarge-zarge.

Asali: Legit.ng

Online view pixel