Innalillahi: Ɗan Majalisar Dokokin Jihar Kano Ya Kwanta Dama da Shekaru 59

Innalillahi: Ɗan Majalisar Dokokin Jihar Kano Ya Kwanta Dama da Shekaru 59

  • An shiga jimami bayan mutuwar ɗan Majalisar dokokin jihar Kano, Halilu Ibrahim Kundila bayan ya sha fama da jinya
  • Marigayin Kundila ya rasu ne a daren jiya Asabar 6 ga watan Afrilu ya na da shekaru 59 a duniya kamar yadda aka tabbatar
  • Wata majiya daga iyalan marigayin ta tabbatar da mutuwar ɗan Majalisar da ya wakilci mazabar Shanono/Bagwai

Abdullahi Abubakar, Editan Legit Hausa ne a bangaren siyasa, kasuwanci da al'amuran yau da kullum ne, ya na da gogewar aikin jarida sama da shekaru uku.

Jihar Kano - Dan majalisar jihar Kano, Halilu Kundila ya riga mu gidan gaskiya ya na da shekaru 59 a duniya.

Marigayin wanda ɗan jami'yyar APC ne ya rasu a jiya Asabar 6 ga watan Afrilu, kamar yadda Punch ta tattaro.

Kara karanta wannan

Karin kudin wuta: Kano da sauran jihohi 12 da suka shirya inganta wuta ga al'ummarsu

Dan Majalisar Kano mai ci ya riga mu gidan gaskiya
Dan Majalisar dokokin jihar Kano, Halilu Kundila ya rasu ya na da shekaru 59. Hoto: Halilu Ibrahim Kundila.
Asali: Facebook

Yaushe aka gudanar da sallar jana'izarsa?

Kundila wanda ya wakilci mazabar Shanono/Bagwai ya rasu ne a daren ranar Asabar 6 ga watan Afrilu bayan ya sha fama da jinya.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Wata majiya daga iyalansa ta tabbatar da cewa an gudanar da sallar jana'izarsa a yau Lahadi 7 ga watan Afrilu a Kundila da ke karamar hukumar Shonono.

"Dan Majalisar ya rasu ne a daren jiya Asabar 6 ga watan Afrilu bayan 'yar gajeruwar jinya an kuma binne shi a garin Kundila."

- Cewar majiyar

Daga cikin wadanda suka halarci jana'izarsa akwai dan Majalisar Tarayya da ke wakiltar Shanono/Bagwai, Yusuf Badau da sauran mambobin Majalisar dokokin jihar.

Marigayi Halilu Kundila ya rasu ya bar mata har guda hudu da kuma 'ya'ya guda 17 a duniya, cewar Daily Post.

Kafin rasuwar marigayin ya raba kayan tallafi a makon da ya gabata domin saukakawa 'yan yankinsa.

Kara karanta wannan

Murna yayin da malamin Musulunci da aka sace a jihar Arewa ya shaki iskar 'yanci

Babban manaja a hukumar NIWA ya rasu

A baya, mun ruwaito muku cewa Babban manajan hulda da jama'a a hukumar kula da hanyoyin ruwa ta Tarayya (NIWA), Dardau Jibril ya riga mu gidan gaskiya.

Dardau ya rasu ne da safiyar ranar Juma'a 5 ga watan Afrilu jim kadan bayan jagorantar sallar asuba a birnin Lokoja da ke jihar Kogi.

Tuni aka gudanar da sallar jana'izarsa bayan kammala sallar Juma'a tare da binne shi a makabartar unguwar Power da ke Lokoja kamar yadda aka sanar tun farko.

Asali: Legit.ng

Authors:
Abdullahi Abubakar avatar

Abdullahi Abubakar (Hausa editor) Marubuci kuma kwararren ɗan jaridan da ya shafe shekaru 3 yana rubutu a fannin siyasa da harkokin yau da kullum. Ya kammala digirin farko a jami'ar Maiduguri. Ya samu horon aikin jarida a Reuters da AFP, ya sha halartar tarukan karawa juna sani game da bincike da adabi. Tuntube shi a abdullahi.abubakar@corp.legit.ng.

Online view pixel