Karin Kudin Wuta: Kano da Sauran Jihohi 12 da Suka Shirya Inganta Wuta Ga Al'ummarsu

Karin Kudin Wuta: Kano da Sauran Jihohi 12 da Suka Shirya Inganta Wuta Ga Al'ummarsu

Yayin da ake ta korafin karin kudin wutar lantarki a Najeriya, wasu jihohi sun shirya ba da ingantacciyar wuta ga alummarsu.

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Abdullahi Abubakar, Editan Legit Hausa ne a bangaren siyasa, kasuwanci da al'amuran yau da kullum ne, ya na da gogewar aikin jarida sama da shekaru uku.

Hakan ya biyo karin kudin wutar da kusan kaso 200 musamman ga wadanda ke rukunin Band A a Najeriya.

Wasu 'yan Najeriya na ganin cewa hakan zai inganta wutar a kasar ganin yadda ake shan fama da matsalar, cewar Thisday.

Kano da sauran jihohi da suka yi alkawarin inganta wuta ga al'ummarsu
Tun bayan kara kudin wuta a Najeriya, Kano da sauran jihohi sun sha alwashin inganta wutar a jihohinsu. Hoto: Uba Sani, Babajide Sanwo-Olu, Abba Kabir.
Asali: Facebook

Jihohin da suka sha alwashin inganta wuta

Legit Hausa ta jero muku jihohin da suka shirya ba da ingantacciyar wuta a jihohinsu.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

1. Kano

Gwamnatin jihar Kano ta bayyana himmatuwarta wurin ba da ingantacciyar wutar ga kamfanoni da al'ummar jihar, cewar Punch.

Kara karanta wannan

Gwamnati ta ce za ta kuma kara kudin wutar lantarki, ta fadi dalili

Daraktan yada labaran gwamnan, Sunusi Dawakin Tofa ya ce gwamnati ta fara aikin inganta wutar a Challawa Goje Tiga shekaru 10 da suka wuce inda ya ce an ci karfin aikin da kaso 90.

2. Nasarawa

Gwamnatin jihar ta bayyana cewa ta yi haɗaka da masu ruwa da tsari a harkar domin samar da wutar a jihar.

Manajan hukumar zuba hannun jari a jihar ta IDA, Ibrahim Abdullahi ya ce sun yi hadakar ce domin inganta tattalin arzikin jihar.

3. Benue

Gwamnatin jihar Benue ta ce shirye-shirye sun kankama domin samar da babban kamfanin rarraba wutar a jihar.

Kwamishinan makamashi, Omale Omale shi ya tabbatar da haka inda ya ce sun kawo tsare-tsare domin inganta wutar a jihar, cewar rahoton Eagles FM.

4. Legas

Kwamishinan yada labarai a jihar, Gbenga Omotosho ya ce Legas ta na kan gaba wurin tabbatar da samar da wutar a jihar.

Kara karanta wannan

Bayan Kaduna, Gwamnan APC ya zargi uban gidansa da yashe lalitar gwamnati gaba ɗaya

Jihar Legas na daya daga cikin jihohin Najeriya da suke fama da matsalar wutar lantarki duk da bunkasar tattalin arziki da suke da shi.

5. Ekiti

Kwamishinan yada labarai a jihar Ekiti, Taiwo Olatunbosun ya ce sun jima da samar da ingantacciyar wuta a jiharsu wanda ke zaman kanta.

Sauran jihohin sun hada da Kaduna da Kebbi da Zamfara da Sokoto da Ondo da Osun da Oyo da kuma Enugu, cewar TheCable.

NERC ta yi karin bayani kan kudin wuya

Kun ji cewa bayan ƙarin kudin wutar lantarki a Najeriya, hukumar NERC ta yi karin haske kan korafe-korafe da ake yi.

Hukumar ta fitar da sanarwa bayan cece-kuce da ake yi kan karin kudin wutar inda ta fayyace wadanda abin ya shafa.

Hakan ya biyo bayan ƙarin kudin wutar da hukumar ta yi da kaso 200 musamman ga wadanda suke rukunin Band A a fadin ƙasar.

Asali: Legit.ng

Online view pixel