Bayanai Sun Fito Yayin da Gwamnoni 2 Su Ka Zauna da Tinubu a Fadar Aso Villa

Bayanai Sun Fito Yayin da Gwamnoni 2 Su Ka Zauna da Tinubu a Fadar Aso Villa

  • Gwamnonin jihohin Neja da Gombe sun ziyarci fadar Aso Rock Villa a karshen makon nan a Abuja
  • Umar Mohammed Bago da Inuwa Yahaya sun samu damar ganin Mai girma Bola Ahmed Tinubu
  • Makasudin zuwan gwamnonin fadar shugaban kasa shi ne ganin yadda za a bunkasa harkar noma

M. Malumfashi ya shafe shekaru ya na kawo labaran Hausa musamman na siyasa, addini, tarihi, wasanni da al’ada.

Abuja - A ranar Alhamis, gwamnan Neja, Umar Mohammed Bago da takwaransa na Gombe, Inuwa Yahaya, su ka je fadar Aso Rock Villa.

Premium Times ta ce gwamnonin jihohin biyu sun gana da Mai girma Bola Ahmed Tinubu a mabanbantan lokuta a fadar shugaban Najeriya.

Bola Tinubu
Bola Tinubu da Gwamnoni Hoto: @Dolusegun16, @InuwaMedia, @HonBago
Asali: Twitter

Bola Ahmed Tinubu da shirin noma

Gwamnonin sun yi magana da shugaba Bola Ahmed Tinubu ne a kan yadda za su hada-kai da gwamnatin tarayya domin a samu abinci.

Kara karanta wannan

Minista ya fadi abin da yake hana Bola Tinubu barci da kyau a Aso Rock Villa

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

A jawabinsa na shiga sabuwar shekara, Bola Tinubu ya nuna muhimmancin yin noma.

Gwamnatin tarayya a karkashin jagorancin Bola Tinubu ta sa ran amfani da eka 500, 000 wajen yin noma a shekarar nan da aka shiga.

A dalilin haka ne gwamna Umar Bago ya ce an tanadi fili a jihar Neja domin noman rani.

Kokarin gwamnan jihar Neja

Gwamnatin jihar Neja ta shiga yarjejeniya da kamfanin Tata Group da hukumar NASENI domin a bunkasa harkar noma a shekarar nan.

Mai girma Umar Bago ya ce idan su ka hada-kai da gwamnatin tarayya, mutanensa za su samar da buhunan abinci kamar yadda ake buri.

...Gwamna Inuwa Yahaya

Rahoton NAN ya ce Inuwa Yahaya ya shaidawa 'yan jarida ya zo ganin shugaban kasa ne domin sanar da shi yadda ake ciki a Gombe.

Kara karanta wannan

Dalilin da yasa ya kamata mata su rika shiga aikin soja, Gwamna Kano Abba Kabir Yusuf

Gwamna Yahaya yake cewa akwai bukatar jiharsa ta hada-kai da gwamnatin tarayya musamman ganin an amince da kasafin kudi.

Gwamnan ya gabatarwa shugaban kasa nasarorin da ya samu a mulki, ya fadi rawan da za su taka domin a noma isasshen kayan abinci.

Tsohon gwamna ya fasa kwai

Kun samu labari an yi wa baitul-mali wayam har ta kai tsohuwar gwamnati tana cin bashi domin a iya biyan albashi, babu komai a asusu.

Cif Segun Osoba ya ce wajibin Bola Ahmed Tinubu ya nemo bashin kudi domin kuwa babu kudin gudanar da ayyuka da ya shiga Aso Villa.

Asali: Legit.ng

Authors:
Muhammad Malumfashi avatar

Muhammad Malumfashi (Hausa writer) M. Malumfashi ya samu Digirin farko a ilmin komfuta a ABU Zaria. Baya ga haka ya yi Digirgir a fannin kula da bayanai da wani Digirgir a ilmin aikin jarida duk daga jami'ar. Malumfashi ya kan kawo labaran siyasa, addini, wasanni da al’ada. Ya halarci taron karawa juna sani iri-iri. Imel: muhammad.malumfashi@corp.legit.ng