Shin Ana Mutuwa a Dawo? Matashin Mawaki Ya Sake Bayyana a Faifan Bidiyo Bayan Sanar da Mutuwarshi
- Shahararren mawaki da ya rasu kwanaki 10 da su ka wuce ya sake bayyana a kafar sadarwa inda ya wallafa bidiyo
- Mawakin wanda aka fi sani da Oladips an sanar da rasuwarshi a ranar 14 ga watan Nuwamba a shafin Instagram
- Abin mamaki, mawakin ya wallafa sabon faifan bidiyo inda ya nuna cewa ya na raye ba kamar yadda aka yada a baya ba cewa ya mutu
Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!
Abdullahi Abubakar, kwararren editan siyasa, kasuwanci da al'amuran yau da kullum ne, ya na da gogewar aikin jarida sama da shekaru uku.
Jihar Legas - Matashin mawaki da ya rasu a kwanakin baya ya sake dawowa bayan bayyanarshi a kafafen sadarwa.
Marigayin mai suna Oladipopu Olabode Oladimeji da aka fi sani da 'Oladips' an sanar da rasuwarshi makwanni kadan da su ka wuce, Legit ta tattaro.
![](https://cdn.legit.ng/images/360x203/cdfa19d15aee3c7f.jpeg?v=1)
Kara karanta wannan
Yadda faston da ke sayar da tikitin shiga aljanna ya gusar da hankulan yayanmu, ya raba mu
![Mawakin Najeriya Oladips ya sake bayyana bayan sanar da mutuwarshi Mawakin Najeriya Oladips ya sake bayyana bayan sanar da mutuwarshi](https://cdn.legit.ng/images/1120/d31f1e1c3cf027b6.jpeg?v=1)
Asali: Instagram
Yaushe aka sanar da mutuwar matashin mawakin?
Manajan kamfaninsa ne ya sanar da mutuwarshi a shafin Instagram a ranar 14 ga watan Nuwamba.
LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng
Daga bisani kamfanin ya goge sanarwar mutuwar mawakin bayan sake bayyanar mawakin a wani sabon faifan bidiyo.
Abin mamaki mawakin ya sake bayyana bayan wallafa wani faifan bidiyo a shafin Instagram a yau Alhamis 23 ga watan Nuwamba.
A cikin faifan bidiyon, an gano shi da mahaifiyarsa inda ya aske kansa sabanin yadda aka sanshi a baya da gashi.
Mahaifiyar mawakin wanda a baya ta hana kai Oladips asibiti an gano ta a bidiyon ta na masa addu'a.
Ku kalli bidiyon a kasa:
Wannan na zuwa ne makwanni kadan bayan mutuwar mawaki Mohbad a jihar Legas wanda ya jawo cece-kuce a Najeriya.
Daga bisani, rundunar 'yan sanda ta tono gawarsa don yin bincike kan musabbin mutuwarshi ganin yadda mutuwar ta ta da jijiyoyin wuya.
![](https://cdn.legit.ng/images/360x203/e1e0bfd019fbcbce.jpeg?v=1)
Kara karanta wannan
Wike zai fatattaki direbobin adaidaita a Abuja daga wata mai kamawa, ya fadi dalili
Matashin mawaki a Najeriya ya riga mu gidan gaskiya
A wani labarin, Matashin mawaki a Najeriya, Oladipopu Olabode Oladimeji ya rasu ya na da shekaru 29 a duniya.
Marigayin wanda aka fi sani da 'Oladips' ya rasu ne a ranar 14 ga watan Nuwamba a Legas.
Wannan na zuwa ne makwanni kadan bayan mutuwar mawaki Mohbad wanda ya rasu shi ma a jihar Legas da aka yi ta cece-kuce.
Asali: Legit.ng