Babban Labari: Gwamnatin Abba Ta Amince da Gina Gadoji da Manyan Ayyuka 15 a Kano

Babban Labari: Gwamnatin Abba Ta Amince da Gina Gadoji da Manyan Ayyuka 15 a Kano

  • Gwamna Abba Kabir Yusuf ya jagoranci zaman majalisar SEC na takwas, watanni hudu bayan ya nada Kwamishinoni a Kano
  • Majalisar zartarwa za ta bada kwangilolin ayyuka da za a aiwatar a kananan hukumomin Birni, Madobi, Kabo da sauransu
  • Gwamnatin Abba za ta biya kudin sayen magunguna a asibitoci kuma za a gina dakin karatun da wuta ta cinye a makaranta

Kano - A karshen zaman majalisar zartarwa ta SEC da gwamnatin jihar Kano ta yi, an amince a yi wasu ayyukan more rayuwa da cigaba.

Mai Girma Gwamna Abba Kabir Yusuf ya sanar da matakin da aka dauka a shafinsa na Twitter a ranar Talata bayan zaman da ya gudana.

Wannan ne karo na takwas da majalisar zartarwa ta yi zama a karkashin Abba Kabir Yusuf.

Kara karanta wannan

Makinde: Gwamnan PDP ya ciri tuta, ya yi ƙarin albashi mai tsoka ga ma'aikata da 'yan fansho

Jerin ayyukan da Abba ya mince da su:

1. Ginin titin kasa da gadar sama a Dangundi a kan N15,974,357,204

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

2. Ginin babbar gadar sama a Tal’udu a kan N15,455,507,265

3. Karin kudin aikin lambatun Jakara zuwa rafin Kwarin Gogau a kan N3,360,084,380

4. Ginin babban titin Kofar Waika-Unguwar Dabai-Yan Kuje a kan N1,579,755,966

5. Ginin gabar titin Unguwa Uku-Yan awaki-Limawa a kan N1,350,460,874

6. Karasa titin Kanye-Kabo-Dugabau a karamar hukumar Kabo a kan N820,262,071

7. Karasa bangaren titin Kofar Dawanau-Kwanar Madugu a kan hanyar Madobi a kan N802,695,617

8. Sake bada kwangilar gadojin tsallaka titi a wurare da-dama a fadin jihar N458,443,067

9. Gyaran wutan kan hanyoyi da na bada hannu a titi a kan N420,000,000

10. Biyan cikon kudin kwangilar gyaran titin Kwanar Kwankwaso a karamar Hukumar Madobi a kan N200,537,271

11. Ayyukan gyara Cibiyar gyaran hali ta Kiru a kan N107,658,976

Kara karanta wannan

Abba v Gawuna: Abubuwa 12 da Kotun Daukaka Kara Za Ta Duba a Shari'ar Zaben gwamnan Kano

12. Sayayyan kaya da magunguna a watan nan, domin bada kula a sassan hadura, agajin gaggawa, juna biyu da kananan yara a kan N53,654,223

13. Biyan kudin magunguna da sinadaran bincike da kayan aiki a asibitin yara na Hasiya Bayero N40,820,564

14. Biyan kason gwamnati wajen aikin rigakafin ‘Diphtheria; a kananan hukumomi 22 a kan N37,005,000

15. Sake gina dakin karatun da ya kone a makarantar koyon shari’a ta Aminu Kano a kan N56,763,475

Nasiru Gawuna v Abba Kabir Yusuf

A labarin shari'a, an ji Nasiru Gawuna ya dauko Ministan shari'a a gwamnatin Olusegun Obasanjo domin ya karbar masa mulkin Kano a Kotu.

Akinlolu Olujinmi, SAN da Wole Olanipekun, SAN suke karawa wajen daukaka karar shari’ar Kano inda ake neman karbe mulki daga hannun NNPP.

Asali: Legit.ng

Authors:
Muhammad Malumfashi avatar

Muhammad Malumfashi (Hausa writer) M. Malumfashi ya samu Digirin farko a ilmin komfuta a ABU Zaria. Baya ga haka ya yi Digirgir a fannin kula da bayanai da wani Digirgir a ilmin aikin jarida duk daga jami'ar. Malumfashi ya kan kawo labaran siyasa, addini, wasanni da al’ada. Ya halarci taron karawa juna sani iri-iri. Imel: muhammad.malumfashi@corp.legit.ng