Kotun Zabe Za Ta Yanke Hukunci Kan Shari'ar Gwamnan Legas a Ranar Litinin

Kotun Zabe Za Ta Yanke Hukunci Kan Shari'ar Gwamnan Legas a Ranar Litinin

  • Kotum da ke sauraron ƙararrakin zaɓen gwamnan jihar Legas ta sanar da ranar yanke hukuncinta
  • Kotun ta bayyana ranar Litinin, 25 ga watan Satumban 2023, a matsayin ranar da za ta yanke hukuncinta kan ƙararrakin da ke gabanta
  • Ƴan takarar jam'iyyun Labour Party da PDP ne dai suka shigar da ƙara a gaban kotun suna ƙalubalantar nasarar da gwamna Sanwo-Olu na APC ya samu

Jihar Legas - Kotun sauraren ƙararrakin zaɓen gwamnan jihar Legas na shirin yanke hukunci kan ƙararrakin da ke ƙalubalantar nasarar gwamna Babajide Sanwo-Olu na jam'iyyar APC a zaɓen ranar 18 ga watan Maris, cewar rahoton PM News.

Ƴan takarar gwamna na jam'iyyar Labour Party (LP), Gbadebo Rhodes-Vivour, da takwaransa na jam'iyyar PDP, Olajide Adediran, wanda aka fi sani da Jandor sune suka shigar ƙararrakin.

Kara karanta wannan

Jerin Sunayen Gwamnonin Jam'iyyar PDP Da Suka Yi Nasara a Kotun Zabe

Kotu za ta yanke hukunci kan shari'ar zaben gwamnan Legas
Kotun za ta zartar da hukuncinta a ranar Litinin, 25 ga watan Satumba Hoto: Governor Sanwo-Olu, Rhodes Vivour
Asali: Facebook

Kotun ta bayyana cewa za ta yanke hukuncin na ta ne a ranar Litinin, 25 ga watan Satumban 2023, rahoton Channels tv ya tabbatar.

Shugaban kotun mai shari'a Arum Ashom, shi ne ya sanar da hakan ga dukkanin ɓangarorin a ranar Asabar, 23 ga watan Satumba.

DUBA: Bibiyemu a Instagram don samun labarai masu muhimmanci kai tsaye cikin manhajar

Menene dalilin shigar da ƙarar?

Rhodes-Vivour da Jandor suna ƙalubalantar ayyana gwamna Babajide Sanwo-Olu da mataimakinsa Obafemi Hamzat na Jam’iyyar APC a matsayin waɗanda suka lashe zaben gwamnan Jihar Legas da hukumar zabe mai zaman kanta ta ƙasa (INEC) ta yi.

Idan ba a manta ba dai a ranar 12 ga watan Agusta, lauyoyin ɓangarorin suka kammala gabatar da bayanansu a gaban kotun.

Hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa INEC ta bayyana Sanwo-Olu na jam’iyyar APC a matsayin wanda ya lashe zaben gwamna da aka gudanar a ranar 18 ga watan Maris.

Kara karanta wannan

Da Dumi-Dumi- Kotun Zabe Ta Yanke Hukunci Kan Nasarar Gwamnan APC a Jihar Arewa

Gwamna Sanwo-Olu dai ya lashe zaɓen da gagarumin rinjaye, inda ya doke Rhodes-Vivour na jam'iyyar Labour Party wanda ya zo na biyu.

Gwamnan ya samu ƙuri’u 762,134 inda ya doke Rhodes-Vivour wanda ya samu ƙuri’u 312,329. Jide Adediran (Jandor) na PDP ya zo na uku inda ya samu ƙuri’u 62,449.

Kotu Ta Tabbatar Da Nasarar Gwamnan APC

A wani labarin kuma, kotun sauraron ƙararrakin zaɓen gwamnan jihar Benue, ta tabbatar da nasarar da gwamna Hyacinth Alia na jam'iyyar APC ya samu a zaɓen gwamnan jihar.

Kotun zaɓen ta yi fatali da ƙarar da jam'iyyar PDP da ɗan takararta Titus Uba suka shigar suna ƙalubalantar nasarar gwamnan.

Asali: Legit.ng

Authors:
Sharif Lawal avatar

Sharif Lawal Sharif Lawal ma'aikacin jarida ne wanda ya samu gogewa a harkar aikin jarida. Ya yi digirinsa na farko a jami'ar Ahmadu Bello (ABU) da ke Zaria. Ya samu horo daga Reuters kan aikin jarida da tantance labarai. Za a iya tuntubarsa ta Sharif.lawal@corp.legit.ng