Manyan Abubuwa 12 Da Suka Faru Tun Lokacin Da Aka Yi Juyin Mulkin Nijar

Manyan Abubuwa 12 Da Suka Faru Tun Lokacin Da Aka Yi Juyin Mulkin Nijar

Niamey, Nijar - A ranar Laraba, 26 ga watan Yuli ne jami'an sojin da ke tsaron fadar shugaban Nijar Muhammed Bazoum, suka kifar da gwamnatinsa.

DUBA NAN: Bibiyi shafin Legit.ng Hausa a kafar TikTok. Kada ka bari bidiyo mai daukar hankali ya wuce ka!

Abdourahmane Tchiani, shugaban dakarun da ke bai wa Bazoum kariya ne ya jagoranci kifar da gwamnatin ta Bazoum.

Hakan ya janyo Allah wadai daga ƙungiyoyi da dama daga sassa daban-daban na duniya.

Abubuwan da suka faru daga juyin mulkin Nijar zuwa yau
Muhimman abubuwa 12 da suka faru daga juyin mulkin Nijar zuwa yau. Hoto: Mahamadou Hamidou/Reuters
Asali: UGC

Daga cikin waɗanda suka nuna adawa da juyin mulkin akwai ƙungiyar raya tattalin ƙasashen Afrika ta Yamma (ECOWAS), wacce ta nemi sojojin na Nijar su mayarwa da Bazoum kujerarsa ba tare da ɓata lokaci ba.

DUBA: Bibiyemu a Instagram don samun labarai masu muhimmanci kai tsaye cikin manhajar

Abubuwa 12 da suka faru daga juyin mulkin na Nijar zuwa yau

Legit.ng ta zaƙulo muhimman abubuwa 12 da suka faru daga lokacin da sojoji suka kifar da gwamnatin farar hula ta Nijar zuwa yanzu kamar yadda Daily Trust ta tattara.

Kara karanta wannan

Yanzu-Yanzu: ECOWAS Ta Sanar Da Ranar Da Za Ta Sake Zama Don Yanke Hukunci Kan Nijar

1. Wa'adin ECOWAS

A ranar Lahadi, 30 ga watan Yuli, shugaban ECOWAS, Bola Ahmed Tinubu, ya bai wa sojojin na Nijar wa'adin kwana bakwai su mayar da mulki.

Sai dai sojojin sun yi burus da wa'adin da aka ba su duk kuwa da barazanar ɗaukar mataki na soji.

2. Rufe iyakoki da katse wuta

Mataki na gaba da Najeriya ta ɗauka shi ne katse wutar lantarkin da take bai wa jamhuriyar ta Nijar.

Haka nan Najeriya ta rufe duka iyakokinta daga shigar da kaya ko fito da su daga Nijar kamar yadda Premium Times ta wallafa.

3. Samun goyon bayan Mali da Burkina Faso

Biyo bayan iƙirarin amfani da ƙarfin sojin da ECOWAS ta yi, ƙasashen Mali da Burkina Faso sun sha alwashin kai wa Nijar ɗauki da zarar an kai ma ta harin.

4. Kwashe 'yan ƙasashen waje

A yayin da abubuwa ke ƙara ɗaukar zafi, manyan ƙasashe irinsu Faransa, Germany da Portugal, sun yi ruguguwar kwashe 'yan ƙasarsu daga Nijar saboda fargabar kada yaƙi ya rutsa da su.

Kara karanta wannan

ECOWAS: Dakarun Mali Da Burkina Faso Sun Isa Jamhuriyar Nijar? Bayanai Sun Fito

5. Amurka ta goyi bayan Tinubu

Ƙasar Amurka ta jinjinawa Shugaba Tinubu bisa matakin da ya ɗauka a matsayinsa na shugaban ECOWAS, inda ta yi alƙawarin ba kawo agaji a duk sanda ake buƙata kamar yadda aka buga a shafin France 24.

6. ECOWAS ta tura wakilci zuwa Nijar

A cikin ƙoƙarin ganin sojoji sun mayar da mulki hannun fararen hula, kungiyar ECOWAS ta tura tawagar sulhu zuwa jamhuriyar Nijar.

Tawagar ta haɗa da Sarkin Musulmi da kuma tsohon shugaban Najeriya Abdulsalami Abubakar, da kuma Omar Alieu Touray.

7. Nuna goyon bayan sojoji

Da dama daga 'yan jamhuriyar ta Nijar, sun cika Niamey wato babban birnin ƙasar, inda suka nuna goyon bayansu ga sojojin da suka gudanar da juyin mulkin.

8. Dakatar da bayar da tallafi

Biyo bayan juyin mulkin, ƙasar Faransa da Germany ta sanar da dakatar da bayar da tallafi ga jamhuriyar ta Nijar.

Kara karanta wannan

Ba Kanwar Lasa: Kididdigar Karfi, Iko da Makamai Tsakanin Sojin Najeriya da Na Nijar

9. Sojojin ECOWAS sun buƙaci a bi matakai na diflomasiyya

Biyo bayan taron da shugabannin tsaron ƙasashen ECOWAS suka gudanar, wanda ya samu halartar ƙasashe 10 daga cikin 15, sun zaɓi bin matakai na diflomasiyya wajen warware rikicin na Nijar.

10. Majalisar Dattawa ta yi fatali da buƙatar Tinubu

A ranar Asabar da ta gabata ne Majalisar Dattawan Najeriya ta sanar da cewa ba ta amince da tura dakarun soji jamhuriyar Nijar ba kamar yadda ECOWAS ta buƙata.

11. Kulle sararin samaniyar Nijar

A ranar Litinin, 7 ga watan Agusta ne sojojin na Nijar suka sanar da kulle sararin samaniyar jamhuriyar Nijar saboda gudun kar a kawo musu hari ta sama kamar yadda Aljazeera ta ruwaito.

12. Nadin Firaminista

Da yammacin ranar Litinin ne sojojin na jamhuriyar Nijar suka sanar da naɗin Ali Mahaman Lamine Zeine a matsayin Firaministan ƙasar.

Shugabannin addinai su gargaɗi Tinubu kan amfani da ƙarfin soji a Nijar

Kara karanta wannan

Shikenan: Sanatocin Najeriya sun yi maganar karshe kan batun tura sojojin Najeriya su yaki na Nijar

Legit.ng a baya ta kawo rahoto kan ƙin amincewa da ƙungiyar jama'atu Nasril Islam ta yi kan shirin da Shugaba Bola Tinubu ke yi na amfani da ƙarfin soji wajen dawo da dimokuraɗiyya a Nijar.

Haka nan ƙungiyar limaman majami'o'i, sun buƙaci Tinubu ya dakatar da shirin da ECOWAS take yi na tura sojoji jamhuriyar Nijar.

Asali: Legit.ng

Authors:
Deen Dabai avatar

Deen Dabai Zaharaddeen Hamisu marubuci kuma ma'aikacin jarida ne da ke da gogewa wajen iya tantance sahihan labarai da na karya. Ya yi digirinsa a jami'ar Ahmadu Bello dake Zaria. Ya samu horo daga Reuters kan aikin jarida da tantance labarai. Baya ga haka, ya shafe sama da shekaru 5 a bangaren aikin watsa labarai wanda hakan ya bashi gogewa ta musamman a aikin jarida. Za a iya tuntubarsa ta adireshinsa na yanar gizo: deen.dabai@corp.legit.ng