An Doke Dangote A Matsayin Wanda Ya Fi Arziki A Afirka A Rahoton Forbes, Dan Afirka Ta Kudu Ya Karbi Matsayin

An Doke Dangote A Matsayin Wanda Ya Fi Arziki A Afirka A Rahoton Forbes, Dan Afirka Ta Kudu Ya Karbi Matsayin

  • Alhaji Aliko Dangote ya rasa matsayinsa na wanda yafi kowa kudi a Nahiyar Afirka gaba daya, a rahoton Forbes da ta cire
  • Dangote ya rasa matakin ne ga wani mai arziki na kasar Afrika ta Kudu, Johann Rupert wanda yanzu shi ne yafi kowa kudi a Nahiyar Afirka
  • Dangote ya rike wannan matsayi na wanda yafi kowa arziki a Nahiyar Afirka fiye da shekaru 10 kafin wannan lokaci da Rupert ya doke shi

Shahararren mai arziki na Najeriya, Alhaji Aliko Dangote ya rasa matsayinsa na wanda yafi kowa kudi a Nahiyar Afirka.

Forbes ta tattaro cewa ya samu raguwar $3.4bn a rana daya saboda faduwar darajar Naira, wanda hakan ya jawo wa masu kudi da dama asara a kasar.

Dangote ya zama na biyu a masu arzikin Nahiyar Afirka
Alhaji Aliko Dangote, Shugaban Kamfanin Dangote. Hoto: Bloomberg.
Asali: Getty Images

Yanzu Aliko Dangote ya sauko mataki na biyu kamar yadda jerin Forbes ya nuna, yayin da attajirin kasar Afirka ta Kudu Johann Rupert ya dare matakin farko.

Kara karanta wannan

Zance ya fito: Bayan Ganawar Tinubu Da Dangote Da Matawalle, Batutuwa Sun Fito Waje

Forbes ta kimanta yawan kudaden Dangote da Rupert

Forbes ta kimanta arzikin Rupert da cewa ya kai $12bn, yayin da 2014 Forbes ta kimanta kudaden Aliko Dangote da cewa ya fi $20bn.

DUBA: Bibiyemu a Instagram don samun labarai masu muhimmanci kai tsaye cikin manhajar

Dangote ya kai shekaru 12 yana rike da kambun wanda yafi kowa arziki a Nahiyar Afirka, cewar Legit.ng.

Rahotanni sun tabbatar da cewa dukiyar Dangote ta ragu daga $25bn a 2014 zuwa $14.2bn saboda matsalolin karyewar darajar Naira a kasuwanni.

Bloomberg ta ce har yanzu Dangote ne mafi arziki a Nahiyar Afirka

Har ila yau, Dangote ne mafi arziki a Nahiyar Afirka a jerin sunayen da Bloomberg ta fitar, amma ya sauko daga cikin mutane 100 mafi arziki a duniya.

Bloomberg ta kimanta arzikin Dangote akan $16.8 a matakin farko yayin da Rupert ta kimanta arzikinsa akan $13.3 a mataki na biyu.

Kara karanta wannan

Abba Gida Gida: Sabon Gwamna Ya Sake Fito da Tsarin Zuwa Jami’o’in Kasashen Waje

Baya ga Dangote, shahararrun masu arziki a Najeriya su ma sun ji wuya dalilin faduwar darajar Naira a kasuwanni.

Wanda yafi kowa kudi a Najeriya bayan Dangote shi ne Abdul Samad Rabiu sai kuma mai biye masa Mike Adenuga.

Dangote, Bill Gates Za Su Gana Da Tinubu A Ranar Litinin

A wani labarin, shugaban kamfanin Dangote, Aliko Dangote ya bayyana ziyarar da za su kawo fadar shugaban kasa, Bola Tinubu.

Dangote ya ce za su kawo ziyarar ne a ranar Litinin 19 ga watan Yuni mai zuwa wurin shugaban kasa.

Ya bayyana haka ne bayan ya yi wata ganawar sirri da Shugaba Bola Tinubu a ranar Juma'a 16 ga watan Yuni.

Asali: Legit.ng

Authors:
Abdullahi Abubakar avatar

Abdullahi Abubakar (Hausa editor) Marubuci kuma kwararren ɗan jaridan da ya shafe shekaru 3 yana rubutu a fannin siyasa da harkokin yau da kullum. Ya kammala digirin farko a jami'ar Maiduguri. Ya samu horon aikin jarida a Reuters da AFP, ya sha halartar tarukan karawa juna sani game da bincike da adabi. Tuntube shi a abdullahi.abubakar@corp.legit.ng.