Jam’iyyar APC Ta Dage Taron Gangaminta Na Shugaban Kasa a Jihar Kwara Saboda Dalili

Jam’iyyar APC Ta Dage Taron Gangaminta Na Shugaban Kasa a Jihar Kwara Saboda Dalili

  • Tawagar kamfen Tinubu ta sanar da dage taron gangamin jam’iyyar a jihar Kwara saboda Buhari zai shilla kasar waje ranar Talata
  • Wannan na zuwa ne a cikin wata sanarwa da APC ta fitar, ta yi karin haske game da dalilin da yasa ta dage taron zuwa gaba
  • Ba wannan ne karon farko da jam’iyyun siyasa ke dage tarukan gangami ba don ba wasu manyan shugabanni damar hakarta

Najeriya - Jam’iyyar APC ta dage taron gangaminta na kamfen din takarar shugaban kasa da ta shirya yi a yau Talata a birnin Ilorin ta jihar Kwara, The Guardian ta ruwaito.

Wannan na zuwa ne a cikin wata sanarwar da kwamitin shirya taron a jihar Kwara ta fitar dauke da sa hannun Saadu Salahu a jiya Litinin 16 ga watan Janairu.

Kara karanta wannan

2023: Dubbannin 'Yan SPW Sun Yanke Shawara, Sun Fadi Wanda Zasu Goyi Baya Tsakanin Tinubu da Atiku

Wannan dage taro dai ya faru ne sakamakon tafiyar da shugaban kasa Muhammadu Buhari zai yi zuwa wata kasar waje a wannan makon.

APC ta dage taron gangaminta a jihar Kwara
Jam’iyyar APC Ta Dage Taron Gangaminta Na Shugaban Kasa a Jihar Kwara Saboda Dalili | Hoto: premiumtimesng.com
Asali: UGC

Sanarwar ta kuma bayyana cewa, shugaban kasa Muhammadu Buhari na da burin jagorantar gangamin na kamfen Tinubu/Shettima da za a gudanar a birnin Ilorin.

DUBA: Bibiyemu a Instagram don samun labarai masu muhimmanci kai tsaye cikin manhajar

Dalili da yasa aka dage taron gangamin

Wani sashenta ya bayyana cewa:

“Muna bakin sanar da dage taron gangamin kamfen Bola Ahmed Tinubu/Shettima na shugaban kasa a APC da aka shirya yi a Ilorin a ranar Talata, 7 ga watan Janairum 2023. An yi hakan ne don ba shugaban kasa Muhammadu Buhari damar jagorantar taron na kamfen.
“Shugaban kasa yana kan wata tafiyar kasa da kasa ta mako guda a wajen Najeriya, farawa daga ranar Talata, amma ya dage yana son da kansa ya jagoranci gangamin APC a Kwara.”

Kara karanta wannan

2023: Bidiyon Yadda Aka Ceci Fitaccen Dan Takarar Shugaban Kasa Daga Tulin Jama'a Ya Fito

Ya zuwa yanzu dai ba a bayyana yaushe ne sabon lokaci da ranar da za a gudanar taron na gangami ba, kamar ydda Premium Times ta ruwaito.

Na Fice Daga APC Ne Domin Gujewa Shugabancin Yaudara, Inji Tsohuwar Shugabar Matan Jam'iyyar

A wani labarin, wata jigo kuma shugabar mata a jam'iyyar APC ta ce babu ita babu maganar a APC a yanzu da nan gaba.

Ta ce ta samu matsuguni mai kyau a jam'iyyar APC, don haka ba za ta taba dawowa APC ba.

A cewarta, akwai mayaudara da masu handama da yawa a jam'iyyar APC, musamman a jiharsu.

Asali: Legit.ng

Online view pixel