Jaruma Rahama Sadau Ta Yi Bikin Cikarta Shekaru 29 a Duniya, Hotunan Sun Ja Hankali

Jaruma Rahama Sadau Ta Yi Bikin Cikarta Shekaru 29 a Duniya, Hotunan Sun Ja Hankali

  • A rana irin ta yau, Laraba, 7 ga watan Disamba aka haifi shahararriyar jarumar fim, Rahama Sadau
  • Rahamah ta yi murnar cikarta shekaru 29 a duniya inda ta saki hadaddun hotunanta a soshiyal midiya
  • Masu amfani da soshiyal midiya sun yi mata fatan alkhairi da addu'a yayin da wasu da dama suka mato kan haduwar da tayi

Fitacciyar jarumar masana’antar shirya fina-finan Kannywood da Nollywood, Rahama Sadau, ta cika shekaru 29 a duniya, a yau Laraba, 7 ga watan Disamba.

Domin raya wannan rana, Rahama ta saki wasu zafafan hotunanta a shafinta na Instagram tana mai nuna farin ciki tsanta.

Rahama Sadau
Jaruma Rahama Sadau Ta Yi Bikin Cikarta Shekaru 29 a Duniya, Hotunan Sun Ja Hankali Hoto: rahamasadau
Asali: Instagram

Rahama ta mika godiyarta ga mahaliccinta

Jarumar ta kuma yi godiya ga Allah Ubangji da ya nuna mata wannan rana a raye kuma cikin koshin lafiya da annashuwa.

Kara karanta wannan

Da Duminsa: Mawaki D’banj ya Shiga Hannun ICPC Kan Zargin Damfarar Miliyoyin N-Power

Shin kana da labarin da ka/ki ke son an wallafa ma ka/ki? Ka tuntubemu a info@corp.legit.ng!

Har ila yau, Rahama ta yi godiya ga Allah a kan ni’imomi da alfarmar da Ya yi mata a rayuwa.

Ta rubuta a shafinta na Instagram:

“SHAFI NA 29 ♂️
“Murna da zagayowar ranar haihuwata,
“Rahama yarinya mai kaunar kanta, karfi, kyau da ban mamaki❤️
“Akwai abubuwan godiya da dama, amma babu wanda ya fi kasancewa a raye, cikin koshin lafiya da farin ciki.
“Alhamdulillah ga wata shekara mai albarka.
“Ya Allah, Nagode da ni’imar da kayi mani ❤️♂️.”

Jama’a sun yi martani

alijita1 ya yi martani:

"Barka da zagayowar ranar haihuwa aminiya."

officialmaryambooth ta ce:

"Barka da zagayowar ranar haihuwa didi❤️."

xeesadau:

"Wannan kyau ne tsantsa na rasa mai zan ce Barka da zagayowar ranar haihuwa masoyiya."

koredebello:

"Barka da zagayowar ranar haihuwa❤️."

aycomedian:

"Barka da zagayowar ranar haihuwa ya @rahamasadau ."

Kara karanta wannan

"Ka Biyo Ni": Wata Dirarriyar Budurwa Ta Nemi Ɗan Acaba Ya Kwanta da Ita, Bidiyon Ya Girgiza Mutane

uzee_usman:

"Barka da zagayowar ranar haihuwa sarauniyar arewa ❤️."

sophiealakija

"Barka da zagayowar ranar haihuwa hadaddiyar sarauniyata "

danielamokachi:

"HBD ALLAH YA MAIMATA MA NA LAFIYA @rahamasadau ."

muh_dk8:

" nima ga karamar kyauta ta Allah yasa batayi kadanba ."

Ango da wani dan gayya sun ba hammata iska a wajen shagalin bikinsa

A wani labari na daban, mun ji cewa wani ango ya dambatu da daya daga cikin mahalarta shagalin bikinsa yayin da mutumin ya yi kokarin manna masa kudi a goshi da sunan liki.

Angon ya cire kudin tare da wurgi da shi amma sai mutumin ya koma ya dauko sannan ya yi kokarin manna masa a karo na biyu lamarin da yasa fada ya kaure a tsakaninsu.

Asali: Legit.ng

Authors:
Aisha Musa avatar

Aisha Musa (Hausa writer) Aisha Musa 'yar jarida ce wacce ta kwashe shekaru biyar tana aikin gogewa a harkar yada labarai. Ta kammala karatun ta a Jami'ar Ibrahim Badamasi Babangida (IBB Lapai) a shekarar 2014 tare da digirin farko a fannin Tarihi. Aisha Editan Hausa ce wacce ke amfani da kwarewa da kwazonta don karfafawa wasu gwiwar yin aiki tukuru don cimma nasara. Ta karbi lambar yabo na gwarzuwar shekarar 2021 a bangaren Hausa na Legit. Za ku iya aika mata sakonnin imel ta adireshinta aisha.musa@corp.legit.ng