Jerin Jihohin Da Ya Wajaba Tinubu Ya Ci Idan Yana Son Nasara A Zaben 2023

Jerin Jihohin Da Ya Wajaba Tinubu Ya Ci Idan Yana Son Nasara A Zaben 2023

Yayinda ake kasa da sauran kwanaki 100 zaben shugaban kasar Najeriya, wani rahoton jaridar ThisDay yayi hasashen jihohin da manyan takara uku ke bukatan ci.

Yan takaran sun hada da Bola Tinubu na APC, Atiku Abubakar na PDP da Peter Obi na LP.

Rahoton ya yi bayanin jihohin da ya wajaba wanda ke son nasara cikin wadannan yan takara uku yayi nasara idan har yana non zama shugaban kasa.

Game da Tinubu, rahoton ya lissafo jerin jihohin da ya wajaba ya samu kashi 60% da kuma 40% da kuma yiwuwan samun hakan.

Shettima
Jerin Jihohin Da Ya Wajaba Tinubu Ya Ci Idan Yana Son Nasara A Zaben 2023 Hoto: APC
Source: Facebook

DUBA: Shigo shafin Legit.ng na manhajar Legit.ng na Telegram! Kada ka bari komai ya wuce ka

Jerin jihohin da ya wajaba Tinubu ya samu akalla 60% idan yana son zama shugaba

Kara karanta wannan

Atiku Butulu Ne, Bai Da Rana: Tinubu Ya Sake Biyowa Ta Kan Abokin Hamayyarsa

Jihohin da Ya Wajaba Tinubu Yaci 60%

Yiwuwan hakan

1

Lagos

Ana Sa rai

2

Ogun

Ana Sa rai

3

Ondo

Ana Sa rai

4

Oyo

Da Yiwuwa (Sai Ya Dage)

5

Osun

Da Yiwuwa

6

Ekiti

Ana Sa rai

7

Kano

Da Yiwuwa (Kamar Wuya)

8

Kaduna

Da Yiwuwa (Sai Ya Dage)

9

Katsina

Da Yiwuwa (Sai Ya Dage)

10

Zamfara

Ana Sa rai

11

Borno

Ana Sa rai

12

Yobe

Ana Sa rai

Jerin jihohin da ya wajaba Tinubu ya samu akalla 40% idan yana son zama shugaba

Jihohin da Ya Wajaba Tinubu Yaci 40%

Yiwuwan hakan

1

Sokoto

Ana Sa rai

2

Kebbi

Ana Sa rai

3

Jigawa

Da Yiwuwa

4

Benue

Da Yiwuwa (Kamar Wuya)

5

Kogi

Ana Sa rai

6

Niger

Ana Sa rai

7

Kwara

Da Yiwuwa

8

Plateau

Da Yiwuwa

9

FCT

Da Yiwuwa

Abin lura: Mafi akasarin jihohin dake karkashin mulkin APC yanzu ake sa ran Tinubu zai samu rinjaye.

Hakazalika Mafi akasarin jihohin dake karkashin mulkin PDP yanzu ake sa ran Tinubu sai ya yi da gaske

Asali: Legit.ng

Authors:
AbdulRahman Rashida avatar

AbdulRahman Rashida