Jerin sunayen yan majalisar dokoki 20 da kotu ta kora kan sauya sheka daga PDP zuwa APC

Jerin sunayen yan majalisar dokoki 20 da kotu ta kora kan sauya sheka daga PDP zuwa APC

Birnin tarayya Abuja - Babbar kotun tarayya da ke zama a Abuja, ta sallami wasu mambobin majalisar dokokin jihar Cross River su 20 a ranar Litinin, 21 ga watan Maris.

Kotu ta kwace kujerun su ne saboda sauya sheka daga jam’iyyar Peoples Democratic Party (PDP) zuwa jam’iyyar All Progressive Congress (APC) mai mulki.

Kotun, a wani hukunci da mai shari’a Taiwo Taiwo ya yanke, ya riki cewa ya zama dole yan majalisar su sauka daga kujerunsu kasancewar sun yi watsi da jam’iyyar da ta dauki nauyin kawo su kan mulki.

Hukuncin ya biyo bayan wata kara mai lamba FHC/ABJ/CS/975/2021, da PDP ta shigar.

Jerin sunaye
Jerin sunayen yan majalisar dokoki 20 da kotu ta kora kan sauya sheka daga PDP zuwa APC Hoto: State Assembly
Asali: Twitter

Shin kana da labarin da ka/ki ke son an wallafa ma ka/ki? Ka tuntubemu a info@corp.legit.ng!

Kara karanta wannan

Da dumi-dumi: Kotu ta kwace kujerun wasu yan majalisa 20 saboda komawa APC

Ga jerin sunayen yan majalisan Cross River 20 da kotu ta fitittika:

1. Michael Ataba

2. Legor Idagbor

3. Eteng Jonnah William

4. Joseph A. Basset

5. Odey Peter Agbe

6. Okon E. Ephraim

7. Regina E. Anyone

8. Matthew S. Olory

9. Ekpo Ekpo Bassey

10.Ogbor Ogbor Udop

11. Ekpe Charles Okon

12. Hillary Ekpang Bisong

13. Francis B. Asuqo

14. Elvert Ayambem

15. Davis Etta

16. Sunday U. Achunekan

17. Cynthia Nkasi

18. Edward Ajang

19. Chris Nja-Mbu Ogar

20. Maria Akawaji

Yan sanda sun karbe majalisar Cross River bayan tsige yan majalisa 20

Jami'an rundunar yan sandan Najeriya sun karbe dukka hanyoyin da ke sada mutum ga harabar majalisar dokokin jihar Cross River.

Sun mamaye wuraren ne tun da misalin karfe 6:00 na asubahi kamar yadda shaidu suka bayyana.

Sashin yan sandan da ke kasa sun hada da na yaki da garkuwa da mutane, masu yaki da kungiyar asiri da kuma jami’an yan sanda na yau da kullum, dukkansu dauke da makamai.

Kara karanta wannan

Jerin abubuwa 8 da Hukumar Kwastam ta hana fitar da su zuwa kasashen waje

The Sun ta kuma rahoto cewa an hangi wasun su na cikin harabar majalisar dokokin.

Asali: Legit.ng

Online view pixel