Kai tsaye: Yadda wasar kwallon AFCON tsakanin Najeriya da Sudan ke gudana

Kai tsaye: Yadda wasar kwallon AFCON tsakanin Najeriya da Sudan ke gudana

Yan kwallon Najeriya Super Eagles zasu buga wasarsu na biyu a gasar kofin nahiyar Afrika tare da yan kwallon kasar Sudan, Falcons.

Za'a buga wannan wasa ne a filin wasan Roume Adjia dake garin Garoua, kasar Kamaru misalin karfe 5 na yamma.

Najeriya ta lallasa kasar Masar a wasarta ta farko da ci guda mai ban haushi.

Ga jerin yan wasan da aka zaba:

Kai tsaye: Yadda wasar kwallon AFCON tsakanin Najeriya da Sudan ke gudana
Kai tsaye: Yadda wasar kwallon AFCON tsakanin Najeriya da Sudan ke gudana
Asali: Twitter

An tashi, Najeriya ta ci Sudan 3-1

Najeriya ta lallasa kasar Sudan a wasar kwallon AFCON da ci uku da daya

Sudan ta samu fenariti, ta rama kwallo guda

Kasar Sudan ta samu zira kwallo guda

Najeriya ta zura kwallo ta uku

Dan kwallon da ya addabi Masar a wasan farko, Moses Simon, ya zura kwallo ta uku

An tafi hutun lokaci, Najeriya na ci 2,0

Yayinda aka tafi hutun lokaci, Najeriya ta zura kwallaye biyu ragar Sudan

Najeriya ta zura kwallo ta biyu

Dan wasan Union Berin a Jamus, Taiwo Awoniyi, ya zurawa Suna kwallo ta biyu

Najeriya ta zura kwallon farko, 1-0

Samuel Chukweze ya zura kwallon farko a daidai minti uku bayan fara wasa

An fara

Kasar Sudan ce ta fara taka leda

Ana dab da farawa, yan wasan Najeriya na motsa jiki

Online view pixel