Sanata Ya Fara Kumfar Baki da Saudiyya, UAE Suka Ki Taya Amurka Yakar Iran
- Sanata Lindsey Graham ya soki abokan hukdartAmurka a yankin Gulf kan kin shiga yaƙin da ake yi da Iran
- Ya nuna rashin jin daɗinsa da matakin UAE na hana amfani da ƙasarta wajen kai hare-hare a kan Iran
- Graham ya kuma soki Spain kan kin barin Amurka ta yi amfani da sansanonin sojinta wajen kai makamantan harin
A'isha Ahmad edita ce a sashen Hausa na Legit. Tana da ƙwarewa wajen rubutun labarai da rahotanni tsawon shekaru uku. Ta kware a kawo rahotannin, al'amuran da su ka shafi mata da yara da siyasa.
United States –Sanata a jam’iyyar Republican a Amurka, Lindsey Graham, ya bukaci abokan hulɗar Amurka a yankin Gulf su ƙara himma wajen goyon bayan ƙasarsa da Isra’ila a rikicin da ke tsakaninsu da Iran.
Graham ya bayyana rashin jin daɗinsa kan yadda wasu ƙasashen da ke kawance da Amurka suka ƙi shiga yaƙin ko kuma bayar da goyon baya kai tsaye.

Source: Facebook
Al-Jazeera ta wallafa cewa Sanatan ya ce matakin da Hadaddiyar Daular Larabawa (UAE) ta ɗauka na hana amfani da ƙasarta wajen kai hare-hare kan Iran ya ba shi takaici matuƙa.
Sanata Amurka ta nemi ɗaukin kasashen Larabawa
Middleeast eye ta ruwaito a cewar Graham, Amurka na bukatar abokan hulɗar da za su iya tashi tsaye su goyi bayan ƙasar a lokacin da ake fama da irin wannan rikici mai muhimmanci.
Ya bayyana mamaki a kan matsayar da ƙasashen suka dauka, inda ya ce za su ga sakamakon rashin taya Amurka da Isra'ila yaki.

Source: Getty Images
Ya ce:
"Muna bukatar abokan hulɗa da za su fito su mara mana baya a yaƙin da ba za mu iya yin sakaci mu yi rashin nasara a ciki ba.”
Sanatan ya ƙara da cewa yana sa ran ƙasashen da Amurka ke abota da su, musamman Saudiyya da sauran ƙasashen yankin Gulf, za su fito su nuna cewa su ma suna da ruwa a cikin wannan rikici.
A cewarsa:
“Ina so abokanmu a Saudiyya da sauran ƙasashe su fito su ce, ‘Wannan fa yaƙina ne ma.’”
Sanatan Amurka ya gorantawa ƙasashen Larabawa
Graham ya kuma tunatar da ƙasashen Larabawa cewa Amurka ta yi ƙoƙari sosai wajen taimaka musu wajen gina sabon tsarin siyasa da tsaro a Gabas ta Tsakiya.
Ya ce:
“Ga abokanmu Larabawa, mum yi ƙoƙari wajen taimaka muku gina sabon Gabas ta Tsakiya. Ya kamata ku ƙara ƙaimi a wannan lokaci.”
Baya ga ƙasashen Gulf, Graham ya kuma soki Spain kan matakin da ta ɗauka na hana Amurka amfani da wasu sansanonin soji da suke tare domin gudanar da yaƙi da Iran.
Spain ta bayyana cewa ba za ta amince a yi amfani da sansanonin sojin da Amurka ke da su a ƙasarta wajen kai hare-hare kan Iran ba.
Graham ya ce wannan mataki ba shi da daɗi daga ƙasar da ake ɗauka a matsayin kawar Amurka.
Saboda haka ya ba da shawarar a mayar da jiragen yaƙin Amurka da ke cikin waɗannan sansanoni zuwa ƙasashen da za su ba su damar amfani da su idan bukatar hakan ta taso.
Sanatan ya ƙara da cewa ya kamata a mayar da jiragen zuwa ƙasar da za ta ba Amurka damar amfani da su idan ta fuskanci barazana daga wata gwamnati irin ta Iran.
Gargadin Amurka ga Iran
A wani labarin, kun ji cewa Shugaban Amurka Donald Trump ya ce sabon jagoran addinin Iran ba zai daɗe a mulki ba idan bai samu amincewar Amurka ba
Donald Trump ya yi zargin cewa Iran na shirin mamaye Gabas ta Tsakiya baki ɗaya yayin da ƙasarsa da Isra'ila suka fara kai mata harin da ya hallaka jagoranta, Ali Khamenei
Shugaban ya kuma ce Amurka ba ta cire yiwuwar tura sojojin musamman domin kwace sinadarin uranium da ake ganin za a iya amfani da shi wajen samar da makamin nukiliya.
Asali: Legit.ng


