Cikakken Sunayen Kasashe 7 da Suka Sassauta Matakan ba da Biza ga 'Yan Najeriya

Cikakken Sunayen Kasashe 7 da Suka Sassauta Matakan ba da Biza ga 'Yan Najeriya

Abuja – Yayin da ’yan Najeriya ke yawan fita ƙasashen waje domin yawon buɗe ido, karatu, da kasuwanci, wasu ƙasashe na duniya sun fara sauƙaƙa musu samun biza da shiga ƙasashensu cikin sauƙ.

Sani Hamza, kwararren edita ne a fannin nishadi, al'amuran yau da kullum da kuma siyasa. Sani yana da shekaru sama da biyar a aikin jarida

Daga Afirka zuwa Gabas ta Tsakiya, gwamnatocin ƙasashe da dama sun fara sassauta dokokin shige da fice, suna ƙara buɗe ƙofofin haɗin gwiwa da Najeriya.

Kasashen duniya 7 sun sassauta matakan ba 'yan Najeriya bizar shiga kasarsu
Hoton Shugaban Najeriya, Bola Ahmed Tinubu da na takardar fasfo na ECOWAS. Hoto: @officialABAT, @ecowas_cedeao
Source: Getty Images

Kasashe 7 sun sassauta samun biza

Ga jerin ƙasashe bakwai da jaridar The Vanguard ta ruwaito cewa sun sauƙaƙa tsarin biza ga ’yan Najeriya.

1. Afirka ta Kudu

Afirka ta Kudu ta ɗauki babban mataki wajen ƙarfafa dangantakarta da Najeriya ta hanyar sauƙaƙa wa matafiya samun biza.

A yanzu, ’yan Najeriya za su iya samun biza ta Afirka ta Kudu ba tare da mika fasfonsu a zahiri ba, abin da ya sauƙaƙa tsarin kuma ya ƙara tsaro, inji rahoton FRCN.

Kara karanta wannan

Jam'iyyar ADC ta kafa sharuda 4 kafin ba 'yan siyasa tikitin takara a 2027

Haka kuma, masu kasuwanci na cin gajiyar bizar ME, wacce za ta ba su damar shiga kasar sau da dama na tsawon shekaru biyar, wanda aka kirkiro domin ƙarfafa zuba jari da cinikayya tsakanin ƙasashen biyu.

2. Hadaddiyar Daular Larabawa (UAE)

Bayan kusan shekaru biyu na takaddama ta diflomasiyya da ta kai ga dakatar da ba 'yan Najeriya biza, ƙasar UAE ta sake buɗe ƙofofinta a 2024, inda ta fara bayar da biza ga ’yan Najeriya.

Jaridar Daily Trust ta rahoto cewa wannan ci gaba ya haɗu da dawowar jiragen Emirates da Etihad da ke zirga-zirga kai tsaye tsakanin Lagos, Abuja, da Dubai bakin aiki.

Ko da yake har yanzu akwai wasu ƙa’idoji ga wasu rukuni na masu neman biza, wannan sauyi ya nuna sahihin haɗin kai da yunƙurin dawo da tsohuwar alakar kasuwanci da yawon shakatawa tsakanin ƙasashen biyu.

3. Kenya

Kenya na ƙara tabbatar da kanta a matsayin ɗaya daga cikin ƙasashen Afirka mafi tsarin yawon buɗe ido ta hanyar soke tsarin izinin tafiya na eTA ga yawancin ’yan Afirka, ciki har da ’yan Najeriya.

Daga Yuli 2025, ’yan Najeriya za su iya shiga Kenya ba tare da biza ba na tsawon kwanaki 90.

Kara karanta wannan

NAHCON ta fitar da sanarwa kan umarnin rage kudin Hajjin 2026 da Tinubu ya yi

Wannan mataki na daga cikin manufofin Pan-African na ƙasar, wanda ke neman ƙarfafa ’yancin zirga-zirga tsakanin ƙasashen Afirka da bunƙasa kasuwanci, yawon buɗe ido, da musayar al’adu.

4. Rwanda

Rwanda na ci gaba da zama abin koyi wajen ƙarfafa haɗin kan Afirka. A yanzu, ’yan Najeriya na iya tafiya Rwanda ba tare da biza ba na tsawon kwanaki 30.

Wannan tsarin yana cikin yunƙurin ƙasar na haɓaka yawon buɗe ido, tarukan kasuwanci, da harkokin kasuwanci tsakanin ƙasashen Afirka.

Babban birnin ƙasar, Kigali, ya zama cibiyar haɗin gwiwa da kirkire-kirkire, yana nuna yadda Afirka za ta kasance a nan gaba.

5. Ghana

BBC ta rahoto cewa Ghana ta rungumi sauyin fasaha a tsarin shige da ficenta ta hanyar ƙirƙirar sabuwar manhajar yanar gizo don neman biza ta intanet.

Tsarin ya kawar da buƙatar takardun hannu da zuwa ofishin jakadanci kai tsaye, inda a yanzu za a iya samun amincewa a cikin ’yan kwanaki kaɗan ta hanyar yanar gizo.

Wannan mataki na ƙara kusantar da haɗin gwiwar ƙasashen yammacin Afirka, musamman tsakanin Accra da Lagos, ta fannin yawon buɗe ido, karatu, da kasuwanci.

Kara karanta wannan

'Domin samun sauki,' Ana neman Tinubu ya saka wa talaka tallafi a abubuwa 3

Kasashen duniya 7 sun sassauta matakan ba 'yan Najeriya bizar shiga kasarsu
Hoton wani bangare na takardar ba da izinin shiga kasa, watau biza. Hoto: Getty Images
Source: Getty Images

6. Barbados

A yankin Caribbean, ƙasar Barbados ta buɗe ƙofofinta ga ’yan Najeriya da sauran ’yan Afirka, inda yanzu suke iya zama har watanni shida ba tare da biza ba.

Wadannan manufofi za su tallafa wa yawon buɗe ido, har ma da ƙarfafa dangantakar tarihi da al’adun da ke tsakanin Afirka da Caribbean.

Haka kuma, ƙasar ta tallata kanta a matsayin wurin da mutane za su iya yin aiki daga nesa daga duk kasashen Afirka ta karkashin shirin WSP.

7. Turkey

Turkiyya ta sauƙaƙa wa ’yan Najeriya da tuni suka mallaki bizar Amurka, Birtaniya, ko Schengen damar samun bizarta cikin sauƙi.

Ta shafin bizarsu na yanar gizo, masu nema na iya cike biza ta intanet kuma su samu amincewa cikin awa 48 ba tare da zuwa ofishin jakadanci ba.

Tsarin ya ƙara ƙarfafa yawon buɗe ido da kasuwanci, yana ba da sauƙin shiga ƙasashen Turai, Gabas ta Tsakiya, da Asiya cikin hanya ɗaya mai dacewa.

Kara karanta wannan

Gwamnatin Kano ta fara binciken Ganduje, an jero zunuban da ake tuhumarsa da su

Tsarin zuwa kasar Norway a saukake

A wani labarin, mun ruwaito cewa, wata ‘yar Najeriya ta ce N170,000 ne za ka biya kudin bizar zuwa Norway, kuma ta fada wa mutane yadda ake samun takardar.

Grandma Shasha ta ce kudin neman bizar kasar Norway bai da tsada, Euro 80 ko N72,000 ne kawai, sannan ba a wani shan wahala wajen samunsa.

Matar ta kara da cewa akwai bukatar mutum ya nuna shaidar yana da kudi, kasuwanci mai rijista ko kuma shaidar takardar aiki domin samun bizar.

Wanda ya tantance Muhammad Malumfashi, babban edita a Legit.ng.

Asali: Legit.ng

Authors:
Sani Hamza avatar

Sani Hamza (Hausa Editor) Sani Hamza ma'aikaci ne da ya yake da gogewa a aikin jarida. Ba fassara labarai da wallafasu a yanar gizo kadai ba, Sani yana da kwarewa a aikin rediyo da talabijin. Ya kuma shafe shekaru 8 a masana'antar fina-finai da dab'i. Imel: sanihamzafuntua@gmail.com