Buhari ya yi ganawar sirri da wasu gwamnoni uku

Buhari ya yi ganawar sirri da wasu gwamnoni uku

Shugaban kasa Muhammadu Buhari ya yi ganawar sirri a lokuta daban-daban da gwamnan jihar Legas; Akinwunmi Ambode, na jihar Kaduna, Malama Nasir El-Rufa'i, da kuma na jihar Benuwe; Samuel Ortom.

Dukkan gwamnoni sun gana ne da Buhari a fadar gwamnatin tarayya dake Abuja a ranar Litinin, 13 ga watan Mayu.

Babu wani jawabi da fito dangane da dalilin ziyarar da gwamnoni suka kai wa Buhari ba, kazalika ba samu labari a kan abinda suka tattauna ba.

Kafin ya karbar bakuncin gwamnonin, Legit.ng ta sanar da ku cewar gwamnan babban bankin kasa (CBN), Godwin Emefiele, ya ziyarci shugaban kasa Muhammadu Buhari a ranar Litinin.

Cikin murmushi da annashuwa, Emefiele ya gaisa da shugaba Buhari a lokacin da shugaban kasa ke taya shi murna.

A cikin satin da ya gabata ne shugaba Buhari ya sake aike wa da sunan Emefiele zuwa majalisa domin sake amince wa da shi a matsayin babban gwamnan CBN a karo na biyu.

A ranar 29 ga watan Mayu ne za a sake rantsar da shugaba Buhari a matsayin zababben shugaban kasar Najeriya a karo na biyu, bayan ya lashe zaben da aka yi a watan Fabarairu.

Shugaba Buhari ya ki bayyana sunayen mutanen da zai bawa mukaman siyasa a sabuwar gwamnatinsa.

Sai dai, hakan bai hana gwamnoni da wasu jiga-jigan 'ya'yan jam'iyyar APC yin zawarcin neman shugaba Buhari ya bawa wasu na hannun daman su ko yaran su mukamai ba.

Muhimmiyar sanarwa: Shafin NAIJ.com Hausa ya koma LEGIT.ng Hausa. Mun gode da kasancewarku tare da mu.

Domin sauke manhajar labaran Legit.ng a wayar ku ta hannu, latsa wannan rubutu na kasa:

https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.android&pid=solomonovlink

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,

Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Authors:
Mudathir Ishaq avatar

Mudathir Ishaq Mudathir Ishaq is the head of the Hausa desk at Legit.ng. He studied Industrial Chemistry as first degree at the University of Abuja, Journalism (CSR Specialization) with the Michigan State University and runs MSc Industrial Chemistry from the Nasarawa State University, Keffi. With more than a decade experience in news reporting and content editing, he has interviewed influential personalities. He can be reached on: mudathir.ishaq@corp.legit.ng