Kwallon Kafa: Lokuta 10 da Matan Najeriya Suka Lashe Kofin Zakarun Afrika

Kwallon Kafa: Lokuta 10 da Matan Najeriya Suka Lashe Kofin Zakarun Afrika

A makon da ya wuce kungiyar 'yan kwallon Najeriya mata (Super Falcons) ta lashe kofin zakarun Afrika karo na 10.

Editan Legit Hausa Ibrahim Yusuf yana da gogewar aikin jarida da rubuce-rubucen adabi sama da shekaru hudu, kuma kwararre ne a kawo rahotannin kasuwanci, siyasa da lamuran yau da kullum.

FCT, Abuja - A makon da ya wuce Najeriya ta kara kafa tarihi bayan lashe gasar kofin zakarun Afrika na mata karon na 10.

'Yan kwallon Najeriya mata da aka sani da Super Falcons sun doke kasar Morocco da ci 3-2 a wasan karshe da aka fafata.

Matan Najeriya suna murna bayan lashe kofin zakarun Afrika
Matan Najeriya suna murna bayan lashe kofin zakarun Afrika. Hoto Getty Images
Source: Getty Images

A wannan rahoton, mun tattaro muku bayanai da tarihin yadda 'yan Super Falcons suka samu nasara har sau 10 a wasan mata 'yan Afrika.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

1. 1998: Farkon nasarar da ta kafa tarihi

The Nation ta rahoto cewa a shekarar 1998 ne Super Falcons suka fara kafa tarihinsu a gasar WAFCON bayan da suka lallasa Ghana da ci 2-0 a wasan karshe.

Kara karanta wannan

Abin mamaki: Farida Sultana da wasu mata 'yan Arewa 2 sun shiga shirin BBNaija

Wannan nasara ce ta farko da ta daukaka sunan Najeriya a kwallon kafa ta mata a nahiyar Afirka da ma duniya baki daya.

Matan Najeriya na murna bayan zuwa kwallo
Matan Najeriya na murna bayan zuwa kwallo. Hoto: Getty Images
Source: Twitter

2. 2000: Najeriya ta kara samun nasara

A gasar 2000 da aka gudanar a Afrika ta Kudu, Super Falcons ta doke kasar a gida da ci 2-0 a wasan karshe.

Wannan ya sa Najeriya ta samu kofinta na biyu a jere, wanda ya karfafa matsayin ta na uwar gasar.

Yan Super Falcons rike da kofin da suka lashe
Yan Super Falcons rike da kofin da suka lashe. Hoto: Getty Images
Source: Twitter

3. 2002: Najeriya ta ci kofin na 3 a jere

Najeriya ta ci gaba da nuna bajintarta a gasar 2002 da aka shirya a Najeriya, inda ta sake doke Ghana da ci 2-0 a wasan karshe.

Wannan ya zama kofinta na uku a jere kuma ya tabbatar da ragamar da suke da ita a gasar tun bayan farawa.

Yan wasan Najeriya suna murnar cin kwallo
Yan wasan Najeriya suna murnar cin kwallo. Hoto: BGetty Images
Source: Twitter

4. 2004: Falcons sun yi nasara karo na 4

A shekarar 2004, Najeriya ta sake zama zakara bayan da ta doke Cameroon da ci 5-0 a wasan karshe.

Wannan babbar nasara ta jaddada yadda Super Falcons ke mamaye gasar da kuma irin karfinsu a filin wasa.

Kara karanta wannan

An fara zanga zangar fatattakar ƴan Najeriya a Ghana, an faɗi laifuffukan da suke aikatawa

Wata 'yar Super Falcons a filin wasa
Wata 'yar Super Falcons a filin wasa. Hoto: Getty Images
Source: Getty Images

5. 2006: Kofi na 5 ya daga darajar Najeriya

A gasar 2006 da aka yi a Najeriya, 'Yan Super Falcons sun doke Senegal a wasan kusa da na karshe sannan suka lallasa Ghana a wasan karshe da ci 1-0.

Duk da cewa a gidan Najeriya aka yi wasan, cin kofin ya nuna karfin da Super Falcons ke da shi a tsawon shekaru.

Magoya bayan Super Falcons a filin wasa
Magoya bayan Super Falcons a filin wasa. Hoto: Getty Images
Source: Getty Images

6. 2010: Super Falcons sun dawo da karfinsu

Bayan an rashin cin nasarar su a 2008, Super Falcons sun dawo da karfinsu a 2010 da aka yi a Afrika ta Kudu.

Sun doke Equatorial Guinea da ci 4-2 a wasan karshe, inda suka kafa sabon tarihi na dawowa da karfi.

Yan wasan Najeriya tare da Bola Tinubu bayan cin kofi na 10.
Yan wasan Najeriya tare da Bola Tinubu bayan cin kofi na 10. Hoto: Bayo Onanuga
Source: Twitter

7. 2014: Najeriya ta lashe kofi na 7

Shafin Statisense ya wallafa a X cewa a gasar 2014 da aka yi a Namibia, Super Falcons sun doke Cameroon da ci 2-0 a wasan karshe da suka buga.

Kara karanta wannan

Za a caɓa: Gwamnatin Tinubu ta fara ɗiban matasa aiki domin rage zaman banza

Wannan karo sun nuna kwarewa, dabaru da hadin kai na gaske, wanda ya basu nasara ba tare da tangarda ba.

Matan Najeriya suna addu'a yayin fara wasa
Matan Najeriya suna addu'a yayin fara wasa. Hoto: Getty Images
Source: Getty Images

8. 2016: Nasara ta 8 a Afrika

Najeriya ta sake lashe kofin a 2016 da aka gudanar a Cameroon, inda ta doke kasar a gida da ci 1-0 a wasan karshe.

Wannan ya zama kofinta na takwas, kuma ya ci gaba da tabbatar da kwarewar Super Falcons a fadin nahiyar Afrika

Wasu 'yan wasan Najeriya a filin wasa
Wasu 'yan wasan Najeriya a filin wasa. Getty Images
Source: Getty Images

9. 2018: Najeriya ta ci kofi na 9

A shekarar 2018, Super Falcons sun lashe kofin bayan sun doke Afrika ta Kudu a bugun finariti 4-3 bayan wasan ya tashi 0-0.

Wannan nasara ta tabbatar da cewa su ne zakarun gasar, kuma daga nan suka fara harin samun kofi karo na 10.

Matan Najeriya yayin da suke buga wani wasa.
Matan Najeriya yayin da suke buga wani wasa. Hoto: Getty Images
Source: Original

10. 2024 (An yi a 2025): Najeriya ta ci kofi na 10

A gasar 2024 da aka buga a 2025 a Morocco, Super Falcons sun doke masu masaukin baki da ci 3-2 a wasan karshe.

Wannan ya zama kofin su na 10 da Super Falcons suka yi burin samu bayan da suka nuna jarunta da kwazo.

Kara karanta wannan

'Wanda ya kamata ya zama ɗan takarar ADC tsakanin Atiku, Obi da Amaechi'

Matan Najeriya na murna baya cin kofi na 10
Matan Najeriya na murna baya cin kofi na 10. Hoto: Getty Images
Source: Twitter

Tinubu ya kalli wasan matan Najeriya

A wani rahoton, kun ji cewa shugaba Bola Ahmed Tinubu ya bayyana cewa ya kalli wasan matan Najeriya da Morocco.

Tinubu ya bayyana cewa bai so kallon wasan ba saboda fargabar hawan jini amma wasu suka kunna talabijin a dakin shi.

Yayin da ya ke karbar 'yan wasan Super Falcons a fadar shugaban kasa, Bola Tinubu ya jinjina musu tare da ba su kyautar makudan kudi.

Wanda ya tantance Muhammad Malumfashi, babban edita a Legit.ng.

Asali: Legit.ng

Authors:
Ibrahim Yusuf avatar

Ibrahim Yusuf (Hausa Editor) Ibrahim Yusuf yana da gogewar aikin jarida da rubuce-rubucen adabi sama da shekaru hudu, kuma kwararre ne a kawo rahotannin kasuwanci, siyasa da lamuran yau da kullum. ibrahim.yusuf@corp.legit.ng