Yanzu Yanzu: Tawagar mata na kungiyar kwallon kafan Najeriya su yi nasarar lashe wasan matan Afrika

Yanzu Yanzu: Tawagar mata na kungiyar kwallon kafan Najeriya su yi nasarar lashe wasan matan Afrika

Kungiyar kwallon kafar Najeriya ta mata (Super Falcons) ta yi nasarar lashe gasar cin kofin kwallon kafa na nahiyar Afrika.

Kungiyar ta samu wannan nasara ne a yau, Asabar, bayan fafatawa a wasan karshe da kasar Afrika ta kudu.

Kungiyar Super Falcons ta samu nasarar zura kwallo 4 a ragar kasar kungiyar Bafana Bafana ta Afrika ta Kudu.

An tashi wasan Najeriya na da kwallo 4 a raga yayin da kasar Afrika ta Kudu ke da kwallo 3 a raga bayan wasan ya shiga karin lokaci.

Yanzu Yanzu: Tawagar mata na kungiyar kwallon kafan Najeriya su yi nasarar lashe wasan matan Afrika
Yanzu Yanzu: Tawagar mata na kungiyar kwallon kafan Najeriya su yi nasarar lashe wasan matan Afrika
Asali: Twitter

Tuni shugaban kasa Muhammadu Buhari ya aike da sakon taya murna ga kungiyar super falcons.

KU KARANTA KUMA: Dan takarar shugaban kasa ya koma APC, ya goyawa Buhari baya

Kazalika, dan takarar shugaban kasa a karkashin inuwar jam'iyyar PDP, Atiku Abubakar, ya taya kungiyar Super Falcons murna.

Wannnan shine karo na 9 da kungiyar super falcons ta lashe gasar cin kofin kwallon kafa na nahiyar Afrika.

Muhimmiyar sanarwa: Shafin NAIJ.com Hausa ya koma LEGIT.ng Hausa. Mun gode da kasancewarku tare da mu.

Latsa wannan domin samun sabuwar manhajar labarai ta Legit.ng Hausa a wayar ku ta hannu: : https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa&hl=en

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari, Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Online view pixel