Shahararrun 'Yan Wasan Kwallon Kafa 8 da Suka Fito daga Arewacin Najeriya

Shahararrun 'Yan Wasan Kwallon Kafa 8 da Suka Fito daga Arewacin Najeriya

Yankin Arewacin Najeriya an san shi da samar da fitattun ƴan wasa waɗanda suka yi suna a harkar ƙwallon ƙafa.

Editan Legit Hausa Sharif Lawal yana da ƙwarewar shekaru wajen kawo rahotannin siyasa, al'amuran yau da kullum, tsegumi da nishaɗi

Ƴan wasan da suke fitowa daga Arewa suna zama zakaru waɗanda ake labarinsu a cikin gida Najeriya da sauran ƙasashen duniya.

Ahmed Musa da fitattun 'yan wasan Arewa
Ahmed Musa na daga cikin fitattun 'yan wasan Arewacin Najeriya Hoto: alhassanyusuf10, zaidu_m3, ahmedmusa718
Asali: Instagram

Jerin fitattun ƴan wasan Arewacin Najeriya

Jaridar Leadership ta tattaro jerin fitattun ƴan wasan ƙwallon ƙafa guda takwas da suka fito daga Arewacin Najeriya waɗanda suka zama sanannu a yanzu.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

1. Ahmed Musa

Ahmed Musa haifaffen birnin Jos ne na jihar Plateau. Ɗan wasan na gaba ya taka leda a kulobluka da dama a ciki da wajen Najeriya

Kara karanta wannan

'Yan sanda sun dakile yunkurin 'yan bindiga na sace mutane a Katsina

Ahmed Musa shi ne ɗan wasan tawagar Super Eagles na farko da ya taɓa cin ƙwallo fiye da ɗaya a gasar cin kofin duniya.

Shi ne kuma ɗan wasan Super Eagles da ya taɓa cin ƙwallo a gasar kofin cin duniya har sau biyu, inda ya zura ƙwallo a gasar ta shekarar 2014 da kuma a gasar ta shekarar 2018, cewar rahoton SportsRation.

2. Umar Sadiq

Umar Sadiq haifaffen jihar Kaduna ne. Yana taka leda a kulob ɗin Real Sociedad na ƙasar Spain.

Ɗan wasan na gaba yana cikin tawagar ƴan wasan Najeriya ƴan ƙasa da shekara 23 da suka lashe tagulla a gasar Olympics ta shekarar 2016.

3. Alhassan Yusuf

Alhassan Yusuf haifaffen jihar Kano ne. Yana taka leda a kulob ɗin New England Revolution da ke ƙasar Amurka

Alhassan yana daga cikin ƴan wasan Super Eagles da suka zo na biyu a gasar AFCON 23 da aka buga a ƙasar Ivory Coast.

Kara karanta wannan

Daga karshe shugaban NLC ya hallara ofishin 'yan sanda, an samu bayanai

4. Zaidu Sanusi

Zaidu Sanusi haifaffen ƙaramar hukumar Jega ne a jihar Kebbi. Yana taka leda a kulob ɗin FC Porto na ƙasar Portugal.

Zaidu yana daga cikin ƴan wasan da ke taka leda a tawagar Super Eagles ta Najeriya.

5. Shehu Abdullahi

Shehu Abdullahi ɗan wasan baya ne wanda aka haifa a jihar Sokoto. Ya taka leda a kulobluka irin su, Kano Pillars da Levski Sofia.

6. Moses Simon

Moses Simon ɗan wasan gaba ne wanda aka haifa birnin Jos na jihar Plateau. Yana taka leda a kulob ɗin Nice na ƙasar France.

7. Jamilu Collins

Jamilu Collins haifaffen jihar Kaduna ne. Ɗan wasan na baya yana taka leda a kulob ɗin Cardiff City na ƙasar Wales.

8. Rabiu Ali

Rabiu Ali yana taka leda a kulob ɗin Kano Pillars a gasar Premier League ta Najeriya.

Rabiu Ali shi ne kyaftin ɗin ƙungiyar kuma ana yi masa kallon ɗaya daga cikin manyan ƴan wasan da kulob ɗin ke alfahari da su.

Kara karanta wannan

'Yan bindiga sun kai hari a Kaduna, sun hallaka jami'in tsaro, ,sun sace manoma

Ronaldo zai yi ritaya daga kwallo

A wani labarin kuma, kun ji cewa gabanin kocin Portugal, Roberto Martinez ya bayyana sunayen 'yan wasansa da za su fafata a gasar 'Nations League,' Cristiano Ronaldo ya bayyana shirinsa na yin ritaya daga ƙwallo.

Tsohon dan wasan na Real Madrid da Manchester United ya ce har yanzu yana son ci gaba da bugawa ƙasarsa wasa amma idan lokacin ritayarsa ya zo, zai tabbata ya shirya.

Muhammad Malumfashi, babban edita a sashen Hausa na Legit ya duba labarin.

Asali: Legit.ng

Authors:
Sharif Lawal avatar

Sharif Lawal Sharif Lawal ma'aikacin jarida ne wanda ya samu gogewa a harkar aikin jarida. Ya yi digirinsa na farko a jami'ar Ahmadu Bello (ABU) da ke Zaria. Ya samu horo daga Reuters kan aikin jarida da tantance labarai. Za a iya tuntubarsa ta Sharif.lawal@corp.legit.ng