Siyasar Najeriya
Abdulmumin Jibrin ya ce idan jam’iyyar NNPP ta hade da LP, Rabiu Kwankwaso za a ba takara. Shi ma Peter Obi zai hakikance a kan shi zai rike tikitin 2023.
Bola Ahmed Tinubu ya halarci bikin taya Femi Gbajabiamila murnar cika 60, Shugaban Majalisa ya yi alkwarin zabawa Tinubu mataimakin da zai ji dadin aiki da shi.
Rudani bisa takamaiman abokin tafiyar 'dan takarar shugaban kasar jam'iyyar APC,Asiwaju Bola Ahmed Tinubu ya cigaba da ta'azzara yayin da yake Abuja don cigaba.
A ranar Lahadin nan ne Yakubu Ajaka ya yi bayanin makomar Jam’iyyar NNPP da takarar Peter Obi da abin da zai faru da Atiku Abubakar a zabe mai zuwa na 2023.
Mataimakin shugaban kasa, Farfesa Yemi Osinbajo ya bayyana cewa zai ci gaba da kasancewa a cikin harkokin siyasan kasar duk da bai samu tikitin jam'iyyar APC.
Ministan shari'a, Abubakar Malami ya bayyana cewa nan ba da dadewa ba kaso 60 cikin dari na mambobin jam’iyyar PDP, za su sauya sheka zuwa APC a jihar Kebbi.
Kungiya ta nuna goyon bayanta ga zabar tsohon kakakin majalisar wakilai Yakubu Dogara, ta ce shine ya fi cancanta ya zama abokin takarar Bola Tinubu a 2023.
Majiyoyi sun bayyana cewa wasu hadiman Osinbajo tare da hadin gwiwar wasu manyan yan siyasar arewa ne ke kokarin ganin an samar da tikitin Osinbajo/Kwankwaso.
Masu neman takarar kujerar gwamna na jam’iyyar All Progressives Congress (APC) a zaben fidda gwanin da aka yi kwanan nan ne suka sauya sheka zuwa jam’iyyar PDP.
Siyasar Najeriya
Samu kari