Masu Garkuwa Da Mutane
Gwamnan jihar Benuwai, Rabaran Hyacinth Alia ya sanar da sa dokar zaman gida a ƙaramar hukumar Ukum da kewaye biyo bayan ɓarkewar zanga-zanga a yankin.
A safiyar yau ne 'yan ta'adda su ka kai hari garin Ayati a karamar hukumar Ukum inda su ka kashe mutane 11 ba haira ba dalili, wannan ja jawo mutane yin zanga-zanga.
Babbar kotun jihar Osun ta yanke hukuncin kisa ta hanyar rataya ga masu garkuwa da mutane da suka kashe wani Bafulatani bayan sun yi garkuwa da shi.
'Yan bindigan da suka sace mahaifiyar Dauda Adamu Kahutu wanda aka fi sani da Rarara sun bukaci a ba su N900m a matsayin kudin fansa kafin su sako ta.
'Yan bindiga sun kai hari gidan wani malamin jami’ar tarayya ta Dutsinma (FUDMA) da ke Katsina. An ce 'yan ta'addan sun kashe malamin, sun kuma tafi da yaransa biyu.
Kimanin matafiya 20 ne rahotanni suka ce wasu ‘yan bindiga sun yi garkuwa da matafiya a kan hanyar Sagamu-Ijebu-Ode a ranar Lahadi da misalin karfe 9 na dare.
An kubutar da mutane biyu da aka yi garkuwa da su a ranar Lahadi bayan wasu ‘yan bindiga sun kai farmaki kauyen Guto da ke Bwari a babban birnin tarayya Abuja.
Yan bindiga sun kai farmaki yankin ƙaramar hukumar Giwa a jihar Kaduna, sun yi awon gaba da dagacin Tunburku, Malam Ashiru da wasu manoma a karshen mako.
Amina Adamu, daya daga cikin matan auren da aka sace su a hanyar Takum-Katsina-Ala a jihar Taraba makonni hudu da suka gabata, ta tsero daga hannun masu garkuwa.
Masu Garkuwa Da Mutane
Samu kari